Ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida ta Jihar Katsina, ta yaba da nasarar aikin hadin gwiwa da dakarun soji na Birgediya 17 tare da hadin gwiwar ‘Air Component Operation Forest Sanity’ suka kai, inda suka yi nasarar ceto mutane 84 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a karamar hukumar Kankara.
Kara karantawaGwamnatin jihar Katsina ta jaddada kudirinta na inganta kanana da matsakaitan masana’antu a fadin jihar.
Kara karantawaGwamnatin tarayya ta sanar da wani shiri na samar da cibiyoyin canza man gas (CNG) da kuma gidajen mai a manyan makarantun gwamnatin tarayya 20 a fadin Najeriya.
Kara karantawaMa’aikatar Ilimi ta Tarayya ta bakin Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a, Boriowo Folasade, ta sanar da kaddamar da wani shiri na koyar da fasaha da koyar da sana’o’in hannu (TVET) a duk fadin kasar domin bunkasa sana’o’i da suka dace da masana’antu a Najeriya.
Kara karantawaKaramin Ministan Ayyuka, Muhammad Goronyo, a wata ziyara da ya kai Katsina a ranar Lahadin da ta gabata, ya bayyana cewa wasu manyan tituna guda biyar a Katsina na daga cikin hanyoyin da gwamnatin tarayya ta yi tanadin kasafin kudi domin kammalawa.
Kara karantawaBabban Daraktan Hukumar Kididdiga ta Jihar Katsina, Farfesa Sani Saifullahi Ibrahim, ya yi alkawarin samar da ingantattun kididdiga na jihar Katsina.
Kara karantawaDakta Abdulhakim Badamasi, likita ne a asibitin koyarwa na gwamnatin tarayya Katsina, ya shawarci jama’a da su rika zuwa asibitin domin duba lafiyar koda a kai a kai domin kaucewa kamuwa da cutar a makara.
Kara karantawaHukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA) ta bai wa kamfanin Max Air damar ci gaba da gudanar da ayyukanta na cikin gida bayan da hukumar ta gudanar da wani bincike mai zurfi kan tsaro da tattalin arziki.
Kara karantawaBabban Alkalin Alkalan Jihar Katsina, Mai Shari’a Musa Danladi Abubakar ya shawarci masu hannu da shuni da su yi amfani da dukiyarsu wajen taimaka wa marayu da marasa galihu a tsakanin al’umma.
Kara karantawaSanarwar da kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya NUJ reshen jihar Katsina ta fitar.
Kara karantawa
