- Ministan ya duba cibiyoyin killace masu cuta, wanke koda (dialysis), da na na’urorin daukar hotunan jiki (imaging)













Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya raka Ministan Lafiya da Jin Dadin Jama’a mai kula da harkokin lafiya (Coordinating Minister), Farfesa Muhammad Ali Pate, da tawagarsa zuwa Asibitin Kwararru na General Amadi Rimi da ke Katsina.
Ministan ya ziyarci cibiyar killace masu cuta ta asibitin, inda Kwamishinan Lafiya na Jihar Katsina, Hon. Musa Adamu, ya zagaya da shi don duba wurin. Ya duba kayan aikin da ke wurin tare da tantance ayyukan da ake gudanarwa a cibiyar.
Haka kuma, Farfesa Pate ya ziyarci Cibiyar Wanke Koda (Dialysis Centre) ta Katsina da kuma Cibiyar Daukar Hotunan Jiki (Imaging Centre) da ake ginawa, inda ya duba kayan aiki da kuma ci gaban ayyukan da ake gudanarwa.
Ministan ya nuna gamsuwa da kayan aikin da ke cibiyar killace masu cuta, tare da yaba kokarin Gwamnatin Jihar Katsina wajen tunkarar matsalolin kiwon lafiya da kuma inganta ayyukan kula da lafiya a jihar.
Daga cikin wadanda suka halarci ziyarar akwai Darakta-Janar kuma Shugaban Hukumar Kula da Inganta Kiwon Lafiya ta Matakin Farko ta Kasa (NPHCDA), Dr. Muyi Aina, da kuma Kwamishinan Lafiya na Jihar Katsina, Hon. Musa Adamu.



