Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya duba sabuwar motar tafi-da-gidanka ta gyaran kayan aikin noma da aka saya domin samar da tallafin fasaha na asali ga shirin jihar na inganta aikin noma ta hanyar amfani da injuna.
Yayin duba motar, Gwamna Radda ya bayyana cewa motar za ta samar da tallafin fasaha da ake buƙata don ƙarfafa shirin jihar na noma na zamani da kuma tabbatar da cewa injunan noma suna ci gaba da aiki yadda ya kamata.
Gwamna Radda ya ce za a ajiye motar ne a Cibiyar Noma ta Zamani ta Jihar Katsina (Katsina State Agricultural Mechanisation Centre), inda za ta yi aiki a matsayin cibiyar gyara ta tafi-da-gidanka domin kula da taraktoci guda 400 da gwamnatinsa ta saya.
Ya bayyana cewa duk lokacin da wani daga cikin taraktocin ya samu matsalar inji a ko’ina a fadin jihar, za a tura motar gyaran daga cibiyar zuwa wurin da matsalar ta faru domin yin gyare-gyaren da suka dace.
Gwamnan ya ce wannan matakin zai taimaka wajen rage lokacin da injuna ke zama a tsaye ba tare da aiki ba, tare da tabbatar da cewa taraktocin suna ci gaba da aiki, musamman a lokutan da ake matuƙar buƙatar su a fannin noma.
Mai kula da Sashen Ci Gaban Noma a Ofishin Gwamna, Dr. Suleiman Umar, wanda ke kula da hukumar KASPA da shirin noma na zamani, ya ce an sayi motar ne domin inganta ƙwarewar fasaha ta maza da mata da ke aiki a fannin noma na zamani a jihar.
Ya ce wannan matakin zai ƙara ƙarfafa kudurin gwamnatin jihar na ganin noma na zamani ya zama abin sha’awa ga manoma, ta yadda za a rage wahalar aikin noma sosai.
Ana sa ran motar gyaran za ta sauƙaƙe yin gyare-gyare a kan lokaci tare da ƙarfafa ƙwarewar fasaha da ake buƙata don dorewar jarin da jihar ta zuba a fannin noma na zamani.
Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai Mataimakin Gwamna, Hon. Faruk Lawal; Shugaban Ma’aikatan Gwamnati (Chief of Staff), Hon. Abdulkadir Mamman Nasir; Kwamishinan Noma, Hon. Aliyu Lawal Shargalle; Manajan Darakta na Hukumar Ci Gaban Ban Ruwa ta Jihar Katsina; da kuma wasu mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar Katsina.








