Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi ta’aziyyar rasuwar Hajia Amina Yahaya Gachi, wacce ta rasu a ranar Litinin tana da shekaru 80 a duniya.
Gwamna Radda ya bayyana cewa Hajia Amina ta yi rayuwa mai cike da ma’ana, wacce aka santa da imani, sadaukarwa, da kuma nuna kauna da taimakon al’umma ta hanyar da ba kasafai ake gani ba.
Ya yi nuni da cewa marigayiyar ta tarbiyyar da ‘ya’ya nagari kuma masu amfani ga al’umma, wadanda ke ba da gudummawa mai muhimmanci wajen ci gaban Jihar Katsina da Najeriya baki daya a fannoni daban-daban kamar aikin gwamnati, aikin injiniya, gine-gine, da sauran fannoni.
A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Katsina, Gwamna Radda ya mika sakon ta’aziyyarsa ta musamman ga daukacin iyalin gidan Yahaya.
Hajia Amina ta bar ‘ya’ya tara, ciki har da Dr. Shamsuddeen Yahaya, Babban Sakatare mai kula da Gyare-gyaren Aikin Gwamnati (Public Service Reforms); Injiniya Yusuf Yahaya, Kodinetan Aiki na Shirin Samar da Hanyoyin Karkara da Tallata Kayayyakin Noma (RAAMP); Architect Zainab Yahaya, Malamar Karatu a Kwalejin Fasaha ta Hassan Usman Katsina (Polytechnic); da Hajia Uwani Yahaya, matar Sarkin Lere, da sauran ‘yan uwanta.
Gwamnan ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta mata kurakuranta, Ya saka mata da alheri, tare da ba ta gidan Aljannatul Firdaus. Haka kuma ya yi addu’ar Allah Ya ba iyalin hakuri da juriya domin jure wannan babban rashi da ba a iya maye gurbinsa.
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
15 ga Satumba, 2026



