Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya kai ziyarar ta’aziyya ga Dr. Yunusa Dankama, Babban Darakta na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta jihar Katsina, bayan rasuwar matarsa da yake kauna, Hajiya Aisha, wacce take da shekaru 46.
Gwamnan ya ziyarci Dr. Dankama a gidansa, inda ya nuna matukar tausayawa kan rashin tare da bayyana marigayiyar a matsayin mace mai nagarta da ta sadaukar da kanta ga iyalinta da al’ummarta.
Gwamna Radda ya yi addu’ar Allah ya gafarta mata kurakuranta, ya ba ta hutun dawwama a Aljannatul Firdaus, sannan ya ba Dr. Dankama da dukkan iyalan karfin jure rashin da ba za a iya gyarawa ba.
Gwamnan ya samu rakiyar Babban Sakataren Gwamnati, Abdullahi Aliyu Turaji, tare da sauran manyan jami’an gwamnati.



