Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina ta dakile harin ‘yan bindiga, ta ceto mutane hudu (4) da aka sace, tare da kwato makamin da suka yi amfani da shi da kuma wasu kayan shaida a Karamar Hukumar Dutsin-Ma.
Kakakin rundunar, DSP Abubakar Aliyu, ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da ya fitar jiya.
A cewarsa, “A ranar 16 ga watan Satumba, 2026, da misalin karfe 12:22 na dare, an samu kiran neman agaji a hedikwatar ‘yan sanda ta yankin Dutsin-Ma, inda aka sanar cewa ‘yan bindiga dauke da makamai sun kai hari kauyen Makwanta tare da sace mata mazauna kauyen su uku.
“Bayan samun rahoton, nan take Babban Jami’in ‘Yan Sanda na yankin (DPO) ya tattara tawagar jami’ai zuwa wurin da lamarin ya faru.
“Tawagar ta bi sawun ‘yan bindigar tare da tare su yayin da suke kokarin tserewa a kan iyakar kananan hukumomin Dutsin-Ma da Danmusa, inda suka yi musayar wuta mai zafi da ‘yan bindigar.
“Ganin karfin makaman ‘yan sandan da kuma dabarunsu, ‘yan bindigar sun tsere zuwa cikin daji tare da raunukan da ake zaton na harbin bindiga ne.
“An samu nasarar ceto dukkan mutane hudu (4) da aka sace ba tare da sun ji rauni ba.”
Ya bayyana sunayen wadanda aka ceton kamar haka: Marawiya Musa (mace, mai shekaru 14); Mariya Ibrahim (mace, mai shekaru 50); Amina Ibrahim (mace, mai shekaru 21); da kuma jariri mai shan nono.
Aliyu ya kara da cewa, yayin gudanar da cikakken bincike a wurin da lamarin ya faru, jami’an ‘yan sandan sun kwato wadannan kayayyaki: Bindiga kirar AK-47 guda daya (1) dauke da harsasai masu rai guda biyar (5); wayar hannu kirar Tecno guda daya (1); na’urorin kunna wakoki (mp3 players) guda uku (3); wuka guda daya (1) da kuma kunshin busassun ganye guda uku (3) da ake zaton tabar wiwi ce.
Ya ce ana ci gaba da kokarin gano tare da cafke wadanda ake zargin da suka tsere.
Aliyu ya kara da cewa, “Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Katsina, CP Ali Umar Fage, ya yaba wa DPO da tawagarsa bisa jajircewarsu, kwarewarsu wajen amfani da dabaru, da kuma gaggawar daukar mataki. Ya sake nanata kudirin rundunar na ci gaba da yaki ba tare da gajiyawa ba kan ayyukan ‘yan bindiga da laifukan tashin hankali a fadin jihar.
“Rundunar tana kira ga al’umma da su ci gaba da kasancewa cikin shiri da kuma bayar da bayanai masu amfani a kan lokaci domin taimaka wa jami’an tsaro wajen…” kare rayuka da dukiyoyi.
“Za a sanar da karin bayanai yayin da bincike ke ci gaba.”



