- An amince da sake gina hanyar Bindawa-Dallaje-Doro-Giremawa-Duwan
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya amince da wani shiri mai girma na tallafawa mata ta fuskar tattalin arziki, wanda zai shafi mata 49,640 a dukkan yankuna (wards) 361 na kananan hukumomin jihar guda 34.
An bayar da amincewar ne a ranar Laraba yayin taro na 16 na Majalisar Zartarwa ta Jihar Katsina, wanda aka gudanar a babban zauren taro na ginin General Muhammadu Buhari (GMB) da ke Katsina, karkashin jagorancin Gwamna Radda.
Da yake yi wa manema labarai bayani bayan taron, Mataimakin Gwamna na Musamman kan Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Injiniya Samaila Inagawa, ya bayyana cewa majalisar ta yi nazari kan takardu da rahotanni daban-daban tare da amincewa da matakan da aka tsara don inganta rayuwa da walwalar al’ummar jihar.
Kwamishiniyar Harkokin Mata, Hajiya Aisha Aminu Malumfashi, ta bayyana cewa shirin zai amfani mata 49,640 a dukkan yankuna 361, inda ake sa ran wadanda za su ci gajiyar shirin za su shiga harkokin kananan sana’o’i da sauran ayyukan samar da kudin shiga.
“An tsara shirin ne domin tallafawa mata wajen karfafa da fadada sana’o’insu, inganta rayuwarsu, da kuma karfafa dogaro da kai ta fuskar tattalin arziki a dukkan kananan hukumomin jihar guda 34,” in ji ta.
Ta bayyana cewa an tsara shirin ne ta yadda zai shafi mata a dukkan yankuna 361 domin tabbatar da cewa sun ci gajiyar wannan tallafi.
A cewarta, tallafawa mata wajen shiga harkokin tattalin arziki zai inganta rayuwar gidaje tare da bunkasa harkokin kasuwanci da tattalin arziki a cikin al’ummomi.
Dangane da batun samar da ababen more rayuwa, Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri, Injiniya Sani Magaji Ingawa, ya bayyana cewa majalisar ta amince da bayar da kwangilar sake gina hanyar Bindawa-Dallaje-Doro-Giremawa-Duwan.
Ya ce aikin zai inganta hanyoyin sadarwa tsakanin al’ummomin da ke kan hanyar tare da saukaka zuwa kasuwanni, asibitoci, makarantu, da sauran muhimman wurare. “Sake gina wannan hanya zai inganta hanyoyin sadarwa, ya saukaka sufuri, tare da samar da ingantacciyar hanyar zuwa kasuwanni, asibitoci, da makarantu ga al’ummomin da ke gefen hanyar,” in ji shi.
Ingawa ya kara da cewa, aikin zai saukaka zirga-zirgar mutane da kayayyaki tare da tallafawa harkokin tattalin arziki a al’ummomin da ke wannan yankin.
Ya ce amincewar ta kara tabbatar da kudirin gwamnati na magance matsalolin muhimman ababen more rayuwa da kuma inganta hanyoyin sadarwa ta fannin hanya a fadin Jihar Katsina.
Mai ba da shawara na musamman kan batun yaran da ba sa zuwa makaranta, Dr. Tasiu Dandagoro, ya bayyana cewa Majalisar ta yi nazari kan wata takardar shawara (memorandum) dangane da bayar da tallafin karatu ga daliban da suka haddace Alkur’ani mai girma.
Dr. Dandagoro ya ce tun da farko Gwamna Radda ya bayar da umarnin samar da tallafin karatu ga daliban da suka haddace Alkur’ani a yayin wani taron tattaunawa da jama’a.
Ya bayyana cewa yanzu an bi diddigin wannan umarni ta hanyar gabatar da takardar shawarar ga Majalisar domin karin nazari.
“Wannan shiri wani bangare ne na kokarin gwamnati na tallafawa daliban da suka nuna kwazo wajen karatun Alkur’ani da kuma karfafa ci gaban ilimi a fadin jihar,” in ji shi.
Matakan da Majalisar ta dauka sun nuna irin muhimmancin da gwamnati ke bai wa batutuwan karfafa tattalin arziki, gina ababen more rayuwa, tallafawa fannin ilimi, da kuma matakan da aka tsara domin inganta rayuwa da walwalar ‘yan kasa a fadin Jihar Katsina.
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
16 ga Satumba, 2026












