- Gwamna ya tabbatar wa al’ummar Yarbawa ci gaba da samun goyon baya da kuma sanya su cikin harkokin jiha
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa dangantakar da ke tsakanin Katsina da yankin Kudu maso Yamma tana da tushe mai karfi a tarihin siyasar Najeriya, inda ya tabbatar wa al’ummar Yarbawa mazauna jihar cewa za su ci gaba da samun goyon baya, da damar shiga harkokin jiha, da kuma kariyar gwamnati.
Gwamna Radda ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis lokacin da ya karbi tawagar Majalisar Al’ummar Yarbawa ta Jihar Katsina, karkashin jagorancin shugabanta, Abdulrazaq Abbas Olukolu, wadanda suka kai masa ziyarar ban girma a zauren taro na ‘Red Chamber’ da ke ginin Muhammadu Buhari House a Katsina.
Gwamnan ya ce dangantakar da ke tsakanin Katsina da mutanen Yarbawa ta wuce batun kabila, harshe, ko yanki, inda ya jaddada cewa bangarorin biyu suna da dadaddiyar alaka ta tarihi, al’adu, da addini.
Ya ce wannan dangantaka ta bayyana karara a tarihin siyasar Najeriya, inda shugabanni daga Katsina da yankin Kudu maso Yamma suka yi aiki tare wajen ciyar da kasar gaba.
Gwamna Radda ya bayar da misali da dangantakar da ke tsakanin tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo da marigayi Janar Shehu Musa Yar’Adua a matsayin misalin alakar kasa da ta wuce iyakar kabila ko yanki.
A cewarsa, tarihin siyasar Najeriya ya nuna cewa fahimtar juna da hadin kai tsakanin yankuna daban-daban na da matukar muhimmanci ga hadin kan kasa da kuma kwanciyar hankalinta.
Gwamnan ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da yanayi mai hada kan jama’a, inda mazauna daga sassa daban-daban na kasar za su iya zama, yin aiki, da kuma bayar da gudummawa wajen ci gaban Katsina.
“Ba na son kalmar nan ta ‘wadanda ba ‘yan asalin wurin ba’ (non-indigenous) idan ana amfani da ita wajen bayyana mutanen da suka shafe shekaru da dama suna zama a wuri guda tare da bayar da gudummawa wajen ci gabansa,” in ji Gwamna Radda.
Ya yi nuni da cewa kaura da alaka tsakanin al’ummomi daban-daban sun kasance wani bangare na tarihin Najeriya, inda ya kara da cewa ‘yan Najeriya da dama suna da asali ko dangantaka da wuraren da suka sha bamban da inda suke zaune a halin yanzu.
“Idan mutum ya shafe shekaru 40 ko fiye yana zama a wuri, sannan a ce masa ‘kai ba dan asalin wurin ba ne,’ ina ganin ya kamata mu tambayi kanmu: wa ne ainihin dan asalin wurin?” in ji shi.
Gwamna Radda ya jaddada cewa bambance-bambancen kabila, harshe, da al’adu bai kamata su raunana hadin kan kasa ko kuma su shafi ainihin kasancewar ‘yan kasa daya ba. “Mu duka ‘yan Najeriya ne, kuma ya kamata mu ci gaba da kallon kanmu a matsayin mutane guda,” in ji shi.
Ya kuma jaddada bukatar sanar da matasa game da bambance-bambancen al’adu na Najeriya, yana mai cewa mu’amala tsakanin al’ummomi daban-daban za ta inganta fahimta da mutunta juna.
Gwamnan ya yaba wa al’ummar Yarbawa bisa goyon bayan da suke bai wa gwamnatinsa da kuma gudummawar da suke bayarwa ga Jihar Katsina.
Ya ba su tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafawa da kare mazauna jihar, ba tare da la’akari da kabila ko yankin da suka fito ba.
Gwamna Radda ya kuma bukaci al’ummar Yarbawa su ci gaba da goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa ana bukatar hadin gwiwa domin ciyar da kasa gaba.
Ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa dangantaka tsakanin Katsina da al’ummar Yarbawa za ta ci gaba da karfafa, tare da yin kira ga mazauna jihar su yi aiki tare domin zaman lafiya, ci gaba, da hadin kan kasa.
“Za mu ci gaba da tallafawa juna. Za mu ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin mutanen da ke zaune a jihar gwargwadon iyawarmu,” in ji shi.
Gwamnan ya kara da cewa mutanen Katsina da takwarorinsu na Yarbawa suna da nauyin da ya rataya a kansu na bayar da gudummawa wajen samar da Najeriya mai karfi.
“Bari mu yi aiki tare domin gina Najeriya mai kyau, Katsina mai kyau, da kuma makoma mai kyau ga dukkan mutanenmu,” in ji Gwamna Radda.
Tun da farko, Shugaban Majalisar Al’ummar Yarbawa, Abdulrazaq Abbas Olukolu, ya gode wa Gwamna Radda bisa karbar tawagarsu da kuma karamcin da ya nuna wa mambobin al’ummar.
Olukolu ya ce ziyarar na da nufin karfafa dangantaka tsakanin al’ummar Yarbawa da Gwamnatin Jihar Katsina.
Ya yaba da salon gwamnan na tafiyar da mulki mai hada kowa da kowa, musamman damar da aka bai wa mutane daga sassa daban-daban na kasar don bayar da gudummawa ga ci gaban jihar.
Shugaban ya ce sanya mambobin al’ummar Yarbawa cikin harkokin gwamnati da aikin gwamnati ya karfafa musu jin cewa su ma ‘yan jihar ne.
“Wannan ya karfafa wa mutanenmu gwiwar kara bayar da gudummawa ga ci gaba da bunkasar Jihar Katsina,” in ji Olukolu.
Ya ba wa gwamnan tabbacin ci gaba da hadin kai da goyon bayan al’ummar, yana mai jaddada cewa mambobinta za su ci gaba da jajircewa wajen zaman lafiya da ci gaban jihar.
Olukolu ya kuma bayyana goyon bayan al’ummar ga Shugaba Tinubu da kuma kokarin gwamnatinsa na ciyar da kasa gaba, da samar da zaman lafiya da hadin kai.
An gudanar da ziyarar ban-girman tare da halartar Shugaban Ma’aikatan Gwamna, Hon. Abdulkadir Mamman Nasir; mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar Katsina; jami’an gwamnati; Masu Ba Gwamna Shawara na Musamman kan Harkokin Wadanda ba ‘Yan Asalin Jihar ba; da kuma shugabanni da mambobin Kungiyar Al’ummar Yarbawa.
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
10 ga Satumba, 2026



















