



Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda ya nuna goyon bayansa ga dan takarar gwamna na APC a zaben Jihar Osun, Asiwaju Munirudeen Bola Oyebamiji.
Radda wanda tare da takwaransa na jihohin Jigawa da Kano, Alhaji Umar Namadi da Abba Kabir suka haɗu da sauran gwamnonin APC a babban taron APC da aka gudanar a Osogbo ranar Alhamis.
Ya yi kira ga mutanen Jihar Osun da su fito kwansu da kwarkwata a ranar Asabar su kaɗa ƙuri’arsu ga APC.



