Gamayyar kungiyoyin farar hula sun roki gwamnatin Katsina da ta sa baki kan jinkirin EHR a cibiyoyin kiwon lafiya na jihar

Da fatan za a raba

Gamayyar kungiyoyin farar hula ta jihar Katsina tayi kira ga Gwamna Dikko Umar Radda kan ya duba yadda za’a inganta tsarin amfani da Internet wajen gudanar da aikace-aikacen kiwon lafiya a manyan asibitocin jihar Katsina.

Wannan na a cikin wata takarda ne mai dauke da Sa Hannun Shugaban Kungiyar Malam Abdul Rahman Abdullahi Dutsinma wanka aka aikoma Madubin Katsina.

A cewar wannan Takarda wannan ya biyo bayan ziyarar gani da ido da gamayyayar kungiyoyin ta kai a wasu asibitocin tare da ganin yadda marassa lafiya ke faman jira a asibitocin kafin su samu kulawa sakamakon tsaiko da akan samu wajen yin amfani da tsarin Internet domin duba lafiyarsu.

Duk da yake akwai amfani da yawa tattare da tsarin wanda kuma yasa dole a jinjina ma gwamnati kan kawo tsarin, Gamayyar kungiyoyin na shawarartar gwamnati da ta duba yadda zata inganta tsarin ta yadda za’a kara karfin Internet din da kuma duba yiwuwar maida tsarin ya yi aiki lokacin da network ya dauke da yadda aikin zai iya hawa idan network ya dawo.

Wannan zai taimaka wajen rage dogon jira da wahalhalun da marassa lafiya ke fuskanta a asibitocin.

  • Labarai masu alaka

    SAMA DA YARA DUBU 29 A KATSINA A KATSINA A CETO YARAN NAN.

    Da fatan za a raba

    A kokarinsa na yaki da jahilci da kuma
    Kungiyar agaji ta Save the Children ta sha alwashin wayar da kan yara sama da 28,000 da ba sa zuwa makaranta a jihar Katsina ta hanyar shirinta na “Ilimi Ba Ya Jira”.

    Kara karantawa

    Rukunnai huɗu na kasafin kuɗi – Yaro

    Da fatan za a raba

    Shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar dokokin jihar Katsina, Alhaji Lawal Haruna Yaro ya ce ginshikan kasafin kudi guda hudu ne.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe
    Jawabin cikin layi
    Duba duk sharhi

    Labarai daga Jihohi

    KW-IRS Ya Kammala Gasar Tambayoyi Tax Club 2025 Matakan Farko

    KW-IRS Ya Kammala Gasar Tambayoyi Tax Club 2025 Matakan Farko

    Hukumar NDLEA ta kama kilo 1.8 na miyagun kwayoyi tare da kama mutane 1,025 da ake zargi a jihar Kwara.

    Hukumar NDLEA ta kama kilo 1.8 na miyagun kwayoyi tare da kama mutane 1,025 da ake zargi a jihar Kwara.
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x