
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana ranakun Juma’a 6 ga watan Yuni da Litinin 9 ga watan Yunin 2025 a matsayin ranakun hutu na bukukuwan Sallah.
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, 2 ga watan Yuni, 2025.
Ya kuma taya al’ummar Musulmi mazauna kasashen waje da kuma fadin Najeriya murnar bikin Sallah.
Ya bukaci al’ummar musulmi da su ci gaba da jajircewa wajen kwadaitar da ruhin sadaukarwa da imani kamar yadda Annabi Ibrahim (A.S) ya yi misali da shi.
Ministan wanda ke dauke da sa hannun babban sakatare na ma’aikatar, Magdalene Ajani, a cikin sanarwar, ya bayyana lokutan Sallah a matsayin lokacin da al’ummar musulmi za su yi wa Nijeriya addu’ar zaman lafiya da ci gaba.
Ya kuma yi wa ‘yan kasar alkawarin cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta himmatu wajen samar da ayyukan da za su dawo da tattalin arzikin Nijeriya da dora al’ummar kasar kan turbar ci gaba.