GWAMNA RADDA ZAI JAGORANCI GWAMNONIN AREWA MASO YAMMA DON NUNA TSARIN YANKIN DA KUMA BUDE KOFAR ZUWAN ZARIN JARIN DUNIYA A TARON GEFE NA UNGA 81
“Daga Yanayin Rashin Kwanciyar Hankali zuwa Damammaki: Hanyoyin da Al’umma ke Jagoranta don Samar da Zaman Lafiya, Juriya, da Zarin Jari a Wuraren da ke da Kalubalen Tsaro”
Gwamnan Jihar Katsina kuma Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, zai jagoranci takwarorinsa daga jihohi bakwai na yankin Arewa Maso Yamma a ranar Litinin, 21 ga Satumba, 2026, zuwa wani muhimmin taron gefe yayin zaman Majalisar Dinkin Duniya na karo na 81 (UNGA 81) a New York.
Taron zai bayyana karuwar rawar da Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma ke takawa a matsayin dandamali na hadin gwiwar yanki, tare da gabatar da Tsarin Zaman Lafiya, Tsaro, da Ci Gaban Arewa Maso Yamma na 2026–2030 ga mahalarta taron daga sassan duniya, wadanda suka hada da abokan huldar ci gaba, masu zarin jari, cibiyoyin hada-hadar kudi, da shugabannin kamfanoni masu zaman kansu.
A cikin kasa da shekaru biyu, kungiyar ta samu ci gaba daga matakin cimma yarjejeniya kan kalubalen da yankin ke fuskanta tare, zuwa matakin amincewa da tsari guda na samar da zaman lafiya, tsaro, juriya, da ci gaba a dukkan jihohi bakwai. Tsarin ya samu goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya, musamman shirin UNDP, tare da ci gaba da sa hannu da goyon baya daga Mataimakiyar Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Mai Girma Amina J. Mohammed.
Ga Gwamna Radda, wannan taro na New York dama ce ta bayyana yankin Arewa Maso Yamma ba wai kawai ta fuskar kalubalen da yake fuskanta ba, a’a, ta fuskar karfin da yankin ke da shi baki daya, da sabbin cibiyoyi, da kuma damammakin zarin jari a fannonin noma, ababen more rayuwa, makamashi, fasaha, hakar ma’adinai, da bunkasa karfin dan adam.
Taron zai kuma neman karfafa hadin gwiwa, samar da kudade, da kuma zarin jari daga kamfanoni masu zaman kansu domin aiwatar da wannan tsari, karkashin taken yankin na: “Jihohi Bakwai. Burin Daya.”
Wannan taro yana wakiltar wani muhimmin sauyi ga kungiyar; daga matakin gina yarjejeniya a matakin yanki zuwa matakin gabatar da tsarin hadin gwiwar Arewa Maso Yamma a fagen duniya.
An sanya hannu:
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
19 ga Satumba, 2026



