Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya amince da bayar da tallafin fara sana’a na Naira miliyan 1 ga kowanne daga cikin ‘yan kasuwar noma 361 da suka kammala horo a rukuni na biyu na shirin ‘Dikko Radda Agripreneurship Training and Empowerment Scheme-Songhai’ (DRATESS-Songhai).
Gwamna Radda ya sanar da wannan tallafi ne a ranar Alhamis yayin bikin kammala horon da aka gudanar a zauren taro na Gidan Gwamnati (Banquet Hall) da ke Katsina, domin wadanda suka samu horo a Cibiyar Horar da Aikin Noma ta Makera Songhai da ke Dutsinma.
Ya bayyana cewa kowanne wanda ya ci gajiyar shirin zai fara karbar Naira 500,000, yayin da za a bayar da sauran kudin a matakai daban-daban dangane da yadda suka kafa tare da gudanar da harkokin kasuwancin noma masu inganci da riba.
Yayin da yake bayyana bikin kammala horon a matsayin babban mataki na sauya fasalin aikin noma daga tsarin dogaro da kai na yau da kullum zuwa tsarin zamani mai dogaro da fasaha da kuma samar da riba, Gwamna Radda ya ce:
“Yau ba bikin bayar da takardun shaida kawai muke yi ba. Biki ne na murnar samun ilimi, bunkasa kwarewa, gina kwarin gwiwa da kuma samar da damammaki,” in ji shi.
Gwamnan ya kara da cewa aikin noma ba wai samar da abinci kawai yake nufi ba. Kasuwanci ne, sana’a ce, damar zuba jari ce, kuma babbar hanya ce ta kawo sauyi a fannin tattalin arziki.
Gwamna Radda ya kara bayyana cewa gwamnatinsa na gina tsarin aikin noma mai inganci, wanda ya dace da yanayi, mai mayar da hankali kan kasuwa da kuma dogaro da kirkire-kirkire; inda ya lura cewa shirin DRATESS-Songhai na bai wa matasa kwarewa ta zahiri a fannonin noman amfanin gona, kiwon dabbobi, kiwon kifi, sarrafa kayan gona, makamashi mai sabuntawa, sake sarrafa shara da kuma kasuwancin noma.
Ya sanar da shirye-shiryen ingantawa da fadada Cibiyar Makera Songhai domin ta rika daukar daliban horo har su kai 1,000 a lokaci guda.
“Ina son ganin wasu daga cikinku sun zama irin su Dangote a nan gaba. Ku yi tunanin da ya wuce na kananan sana’o’i kawai. Ku kafa kamfanoni ko harkokin kasuwanci da za su samar da ayyukan yi tare da kawo sauyi a al’ummominku,” in ji Gwamna Radda ga wadanda suka kammala horon.
“Kada ku ajiye takardun shaidarku a jikin bango kawai kuna jiran aikin gwamnati. Ku mayar da kwarewarku ta zama sana’o’i, sannan ku mayar da sana’o’inku su zama damammaki ga wasu,” in ji Gwamna Gwamnan.
Ya kuma bayyana cewa daya daga cikin kalubalen da ke gaban gwamnatin shi ne yadda za a mayar da dumbin albarkatun noma zuwa damammakin tattalin arziki masu dorewa. “Kuna da muhimmiyar rawar da za ku taka a wannan sauyi. Ina son ganin kun mayar da gonaki su zama sana’o’i, sana’o’i su zama masana’antu, sannan masana’antu su zama hanyoyin samar da damammaki ga al’ummarmu,” in ji shi.
Gwamna Radda ya tabbatar wa wadanda suka kammala horon cewa za a ci gaba da hada su da cibiyoyin hada-hadar kudi, masu zuba jari, kasuwanni, da shirye-shiryen ci gaba, tare da karfafa musu gwiwar ci gaba da gudanar da kungiyoyin hadin gwiwa domin samun saukin kudi da kasuwanni.
Da farko, Kodinetan Sashen Shirye-shiryen Ci Gaban Aikin Gona (ADPU), Dr. Suleiman Umar, ya bayyana cewa an tsara shirin DRATESS-Songhai ne a matsayin hanyar da za ta kai mutum daga matakin horo zuwa kafa sana’a, samar da kudin shiga, da samar da ayyukan yi.
“DRATESS-Songhai ya wuce tsarin horo kawai; shiri ne na zuba jari a kan karfin dan adam, tabbatar da wadatar abinci, inganta yawan amfanin gona, da kuma makomar tattalin arzikin Jihar Katsina,” in ji Dr. Umar.
Ya bayyana cewa matasa 361 ne suka kammala horo a rukuni na biyu, bayan an fara da rukuni na farko mai mutane 102, yayin da wasu matasa 361 ke ci gaba da samun horo a halin yanzu. Ya yi bayanin cewa shirin, wanda ke daukar watanni shida, ya kunshi koyarwa a aji da kuma horon aiki a fili, tare da samar da masauki, abinci sau uku a rana, wuraren wasanni da nishadi, da kuma alawus na Naira 30,000 a kowane wata.
A jawabinsa, Kwamishinan Aikin Gona, Hon. Aliyu Lawal Shargalle, ya yaba wa Gwamna Radda bisa zuba jari a fannin horar da matasa aikin gona na zahiri da kuma karfafa gwiwarsu, inda ya bayyana DRATESS-Songhai a matsayin muhimmin shiri na samar da kwararrun ma’aikata da za su zamantar da aikin gona tare da karfafa tsaron samar da abinci.
Darakta-Janar na Hukumar Ci Gaban Sana’o’i ta Jihar Katsina (KASEDA), Dr. Babangida Ruma, ya yi alkawarin ci gaba da hadin gwiwa tare da tabbatar wa wadanda suka ci gajiyar shirin cewa KASEDA za ta taimaka wajen yin rajistar sana’o’insu a Hukumar Kula da Kamfanoni (CAC) domin saukaka musu samun kudi da kasuwanni.
Da suke magana a madadin wadanda suka kammala horon, Hamza Yahaya da Fatima Babangida sun nuna godiyarsu ga Gwamna Radda da Gwamnatin Jihar Katsina bisa horon aiki, masauki, abinci, alawus, da sauran tallafin da aka ba su, tare da yin alkawarin yin amfani da ilimi da kwarewar da suka samu wajen kafa sana’o’i masu inganci da kuma bayar da gudummawa ga ci gaban tattalin arzikin jihar. Taron ya samu halartar mataimakin gwamna Malam Faruk Lawal Jobe, shugaban ma’aikata Alhaji Murtala Banye, shugaban ma’aikata Alhaji Abdulkadir Mamman Nasir, yan majalisar zartarwa na jiha, shugabannin MDAs, shugabannin gargajiya da na addini.
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
17 ga Satumba, 2026



