Shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) kuma Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya taya Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, murnar cika shekaru 57 da haihuwa.
A cikin sakon taya murna mai dauke da kwanan watan 10 ga Satumba, 2026, AbdulRazaq ya isar da sakon taya murna na musamman daga Kungiyar Gwamnonin Najeriya zuwa ga Gwamna Radda, inda ya bayyana wannan rana a matsayin damar yin bikin tunawa da sadaukarwarsa da kuma salon jagorancinsa.
Shugaban na NGF ya jinjinawa Gwamna Radda musamman kan jajircewarsa da kuma kudirinsa na ganin an samu ci gaba da bunkasar Jihar Katsina da ma Najeriya baki daya.
“A yau, ba wai kawai muna bikin cika wata shekara a rayuwarka ba ne, har ma muna bikin sadaukarwarka, jagorancinka, da kuma jajircewarka wajen ganin an samu ci gaba da bunkasar Jihar Katsina da kasarmu baki daya,” in ji AbdulRazaq.
Ya yi addu’ar samun lafiya, karin karfi, da kuma samun gagarumar nasara ga Gwamnan na Katsina, tare da fatan cewa shekaru masu zuwa za su zo da karin nasarori masu tasiri da kuma hikima wajen yi wa al’umma hidima.
Har ila yau, AbdulRazaq ya yi wa Gwamna Radda fatan ganin ya cimma dukkan manufofinsa da burinsa na ganin ci gaban Jihar Katsina da kuma al’ummar da yake yi wa hidima.
Wannan sako ya zo ne a matsayin karin sakon fatan alheri ga Gwamna Radda dangane da zagayowar ranar haihuwarsa, wanda ke nuna yadda ake yaba salon jagorancinsa da kuma jajircewarsa wajen yi wa jama’a hidima.
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
10 ga Satumba, 2026



