Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya karbi bakuncin dan takarar Daura/Sandamu/Mai’adua, Hon. Yusuf Muhammadu Buhari, wanda ya gabatar da fom din tsayawa takara da kuma nuna sha’awar sa ga gwamnan a fadar gwamnati dake Katsina.
Wadanda suka halarci taron sun hada da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin siyasa, Ibrahim Kabiru Masari; Kodinetan kungiyar AUDA-NEPAD na kasa, Hon. Jabiru Tsauri; da sauran masu ruwa da tsaki daga mazabar.



