Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina ta dakile yunkurin satar shanu, inda ta kama wani da ake zargi da satar shanu tare da kwato dabbobi guda hamsin (50) da aka sace.
Kakakin rundunar, DSP Abubakar Aliyu, ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Katsina ranar Lahadi.
Aliyu ya bayyana cikakkun bayanai kamar haka: “A ranar 12 ga watan Satumba, 2026, da misalin karfe 7:30 na dare, an samu kiran gaggawa daga wani mutum mai kishin kasa yana sanar da cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne dauke da muggan makamai sun kai hari kauyen Kwarara da ke Karamar Hukumar Jibia, inda suka sace dabbobi.
” Bayan samun rahoton, nan take Babban Jami’in ‘Yan Sanda na Jibia (DPO) ya tattara tawagar sintiri ta VCRU tare da hadin gwiwar Rundunar Tsaro ta Al’umma ta Jihar Katsina (KSCWC) suka nufi wurin da lamarin ya faru.
” Tawagar ta bi sawun ‘yan bindigar cikin dabara kuma ta tare su a yankin madatsar ruwa ta Jibia, inda aka yi musayar wuta.
Sakamakon karfin ikon wutar ‘yan sandan, ‘yan bindigar sun yi watsi da dabbobin da suka sace sannan suka tsere daga wurin dauke da raunukan harbin bindiga daban-daban.
” A yayin binciken wurin, an kama mutum daya (1) da ake zargi da satar shanu, mai suna Ibrahim, wanda aka fi sani da “Daura” (namiji, mai shekaru 22). An samu nasarar kwato jimillar dabbobi 50 da aka sace, wadanda suka hada da shanu goma sha biyar (15) da tumaki talatin da biyar (35).
” A yanzu haka wanda ake zargin yana hannun ‘yan sanda, inda yake ba da hadin kai ga binciken da ake gudanarwa domin gano tare da kama sauran ‘yan kungiyar da suka tsere.
” Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Katsina, CP Ali Umar Fage, ya yaba wa DPO na Jibia da tawagarsa ta musamman bisa nuna jaruntaka da kuma daukar mataki cikin gaggawa.
” Ya sake jaddada kudirin rundunar na kawar da masu aikata laifuka daga jihar tare da yin kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa rundunar bayanai masu inganci a kan lokaci.”



