An ruwaito cewa wasu da ake zargin ‘yan fashi ne suka sace Manjo Janar Rabe Abubakar (mai ritaya), tsohon Daraktan Yada Labarai na Tsaro da matarsa, a kan hanyar Matazu ta Jihar Katsina.
A cewar bayanai da manema labarai suka samu, babban jami’in soja mai ritaya da matarsa suna tafiya zuwa Jihar Katsina lokacin da wasu masu dauke da makamai suka tare su suka tafi da su ranar Asabar.
Wata majiya ta ce direban janar mai ritaya ya samu nasarar tserewa daga wurin duk da raunin harbin bindiga a lokacin harin.
Majiya ta kara da cewa an gano motar da ke cikin lamarin, wacce aka bayyana a matsayin jan Peugeot 504 da aka bai wa babban jami’in, daga baya kuma an ajiye ta a hedikwatar rundunar ‘yan sandan Najeriya ta Matazu.
Har zuwa lokacin da ake gabatar da wannan rahoton, rundunar ‘yan sandan jihar Katsina da hukumomin soji ba su fitar da wata sanarwa a hukumance da ke tabbatar ko musanta labarin sace shi ba.



