







Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, tare da mataimakin gwamna Hon. Malam Faruk Lawal, ya bi sahun daruruwan al’ummar musulmi wajen sallar jana’izar marigayiya Hajiya Laila Yunusa.
An yi Sallar Jana’izar ne a jiya a Masallacin Juma’a na Banu Commassie da ke Katsina.
Hajiya Laila Yunusa, mai shekaru 87, ta kasance mahaifiyar Ambasada Hussaini Commassie, shugaban ofishin jakadanci a Najeriya, hukumar zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya.
Gwamna Radda ya yi addu’ar Allah ya jikan marigayiyar, ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da ya jikanta da Aljannatul Firdaus, sannan ya bukaci ‘yan uwa da su yi hakuri da Imani.



