







Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, jim kadan bayan taron jam’iyyar APC na shiyyar Arewa maso Yamma, ya ziyarci Asibitin tunawa da Yusuf Dantsoho da ke Tudun Wada Kaduna domin duba wakilan jam’iyyar APC daga karamar hukumar Sabuwa wadanda suka yi hatsarin mota yayin da suke tafiya zuwa wurin taron.
Lamarin ya yi sanadiyyar mutuwar Dalhat Machika.
Daga cikin wadanda hatsarin ya rutsa da su akwai tsohon mataimakin gwamna, Hon. Sirajo Umar Damari, da kuma shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Sabuwa. A halin yanzu suna karbar magani a asibiti.
Gwamna Radda ya tausaya wa wadanda abin ya shafa da iyalansu, ya yi musu addu’ar samun sauki cikin gaggawa, sannan ya tabbatar musu da goyon bayan gwamnati a wannan mawuyacin lokaci.
Gwamnan ya samu rakiyar mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin siyasa, Hon. Ibrahim Kabir Masari; shugaban ma’aikatan gwamna, Hon. Abdulkadir Mamman Nasir; da sauran manyan jami’an gwamnati.



