Majalisar dokokin jihar Jigawa ta amince da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 ya zama doka

Da fatan za a raba

Majalisar dokokin jihar Jigawa ta amince da kudurin kasafin kudi na shekarar 2025 na sama da naira biliyan 698 na ayyukan gwamnatin jihar da kuma naira biliyan 184 na ayyukan kananan hukumomi 27.

Hakan ya biyo bayan gabatarwa da kuma amincewa da rahoton zaunannen kwamitin kasafin kudi na majalisar.

Da yake gabatar da rahotan shugaban kwamitin wanda shi ne mamba mai wakiltar mazabar Malam Madori, Alhaji Hamza Adamu Ibrahim ya bayyana cewa dukkanin kwamitocin majalisar sun tantance tanade-tanaden kasafin kowace ma’aikatar da hukumar domin yin gyara ko kari a cikin kasafin kudin.

A cewarsa, kwamitocin sun kuma yi da masu ruwa da tsaki daban-daban da suka hada da kungiyoyin farar hula tare da gudanar da aikin tantancewa a kokarin da ake na isa ga wani cikakken daftarin kasafin kudi domin gabatar da shi ga zaman majalisar.

Bayan amincewar baki daya ta hanyar kada kuri’a, kakakin majalisar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya sanar da amincewa da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 ya zama doka.

  • Labarai masu alaka

    KTSG Ta Ƙarfafa Maganin Ciwon Diphtheria, Ta Yi Allurar Rigakafi Sama da 150,000 Cikin Kwanaki 5

    Da fatan za a raba

    Gwamnatin Jihar Katsina ta ƙara tsaurara matakai don dakile barkewar cutar diphtheria a jihar, inda ta yi wa mutane sama da 150,000 allurar riga-kafi a cikin kwanaki 5 na farko na yaƙin neman zaɓen gaggawa.

    Kara karantawa

    Shugaban ‘yan ta’adda ya tsere da raunukan harbin bindiga inda ya rasa kwamandojinsa guda biyu

    Da fatan za a raba

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na rundunar hadin gwiwa ta Arewa maso Yamma, Operation Fansan Yamma, sun kashe manyan kwamandoji biyu na wata kungiyar ‘yan ta’adda a lokacin wani samame da jami’an leken asiri suka kai a karamar hukumar Matazu ta jihar Katsina.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe

    Labarai daga Jihohi

    ‘Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi A Kan Iyakar Zamfara da Katsina Da Harsasai 800 AK-47 A Cikin Tankin Mai Na Babura

    ‘Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi A Kan Iyakar Zamfara da Katsina Da Harsasai 800 AK-47 A Cikin Tankin Mai Na Babura

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x