Majalisar dokokin jihar Jigawa ta amince da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 ya zama doka

Da fatan za a raba

Majalisar dokokin jihar Jigawa ta amince da kudurin kasafin kudi na shekarar 2025 na sama da naira biliyan 698 na ayyukan gwamnatin jihar da kuma naira biliyan 184 na ayyukan kananan hukumomi 27.

Hakan ya biyo bayan gabatarwa da kuma amincewa da rahoton zaunannen kwamitin kasafin kudi na majalisar.

Da yake gabatar da rahotan shugaban kwamitin wanda shi ne mamba mai wakiltar mazabar Malam Madori, Alhaji Hamza Adamu Ibrahim ya bayyana cewa dukkanin kwamitocin majalisar sun tantance tanade-tanaden kasafin kowace ma’aikatar da hukumar domin yin gyara ko kari a cikin kasafin kudin.

A cewarsa, kwamitocin sun kuma yi da masu ruwa da tsaki daban-daban da suka hada da kungiyoyin farar hula tare da gudanar da aikin tantancewa a kokarin da ake na isa ga wani cikakken daftarin kasafin kudi domin gabatar da shi ga zaman majalisar.

Bayan amincewar baki daya ta hanyar kada kuri’a, kakakin majalisar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya sanar da amincewa da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 ya zama doka.

  • Labarai masu alaka

    FG ta ayyana Ranar Juma’a da Litinin ga Jama’a don Bukin Sallar Idi

    Da fatan za a raba

    Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana ranakun Juma’a 6 ga watan Yuni da Litinin 9 ga watan Yunin 2025 a matsayin ranakun hutu na bukukuwan Sallah.

    Kara karantawa

    KUNGIYAR KWALLON KAFA TA JIHAR KATSINA DA HUKUMAR KWALLON KAFA DA GWAMNATIN JAHAR KANO.

    Da fatan za a raba

    Kungiyar kwallon kafa ta jihar Katsina (F.A) ta bayyana kaduwarta dangane da rasuwar wasu ‘yan wasa da jami’ai da ‘yan jarida daga jihar Kano da ke dawowa gida bayan halartar bikin wasannin kasa da aka kammala a jihar Ogun.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe
    Jawabin cikin layi
    Duba duk sharhi

    Labarai daga Jihohi

    An Bukaci Mazauna Al’ummar Ira Da Su Bada Goyon Bayan Yaki Da FGM A Kwara

    An Bukaci Mazauna Al’ummar Ira Da Su Bada Goyon Bayan Yaki Da FGM A Kwara

    Dan Majalisa Yayi Kira Ga Jiha Da FG Domin Ceton Mazaunan Edu, Moro Da Patigi LG Daga Hari

    Dan Majalisa Yayi Kira Ga Jiha Da FG Domin Ceton Mazaunan Edu, Moro Da Patigi LG Daga Hari
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x