Majalisar dokokin jihar Jigawa ta amince da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 ya zama doka

Da fatan za a raba

Majalisar dokokin jihar Jigawa ta amince da kudurin kasafin kudi na shekarar 2025 na sama da naira biliyan 698 na ayyukan gwamnatin jihar da kuma naira biliyan 184 na ayyukan kananan hukumomi 27.

Hakan ya biyo bayan gabatarwa da kuma amincewa da rahoton zaunannen kwamitin kasafin kudi na majalisar.

Da yake gabatar da rahotan shugaban kwamitin wanda shi ne mamba mai wakiltar mazabar Malam Madori, Alhaji Hamza Adamu Ibrahim ya bayyana cewa dukkanin kwamitocin majalisar sun tantance tanade-tanaden kasafin kowace ma’aikatar da hukumar domin yin gyara ko kari a cikin kasafin kudin.

A cewarsa, kwamitocin sun kuma yi da masu ruwa da tsaki daban-daban da suka hada da kungiyoyin farar hula tare da gudanar da aikin tantancewa a kokarin da ake na isa ga wani cikakken daftarin kasafin kudi domin gabatar da shi ga zaman majalisar.

Bayan amincewar baki daya ta hanyar kada kuri’a, kakakin majalisar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya sanar da amincewa da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 ya zama doka.

  • Labarai masu alaka

    ‘Katsina Ta Bada Ɗaya Daga Cikin Muhalli Mafi Kyau Na Nijeriya Don Zuba Jari Da Haɗin Gwiwa’ – Gwamna Radda Ga Wakilan Tarayyar Turai

    Da fatan za a raba

    Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, CON, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta himmatu wajen gina gwamnati mai haɗa kai da kuma samar da yanayi mai kyau don ci gaba mai ɗorewa da ci gaban tattalin arziki.

    Kara karantawa

    Labaran Hoto: Gwamna Radda Ya Kai Wa Jakadun Tarayyar Turai Ziyarar Tarihi Kan Rijiyar Kusugu Mai Shekaru 2,005

    Da fatan za a raba

    Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, a ranar Asabar ya jagoranci jakadun Tarayyar Turai goma sha bakwai zuwa wata ziyara a tsohuwar Rijiyar Kusugu da ke Daura a matsayin wani bangare na ayyukan bikin Eid-el-Fitr na shekarar 2026 a jihar.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe
    Jawabin cikin layi
    Duba duk sharhi

    Labarai daga Jihohi

    ‘Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi A Kan Iyakar Zamfara da Katsina Da Harsasai 800 AK-47 A Cikin Tankin Mai Na Babura

    ‘Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi A Kan Iyakar Zamfara da Katsina Da Harsasai 800 AK-47 A Cikin Tankin Mai Na Babura

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x