Majalisar dokokin jihar Jigawa ta amince da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 ya zama doka

Da fatan za a raba

Majalisar dokokin jihar Jigawa ta amince da kudurin kasafin kudi na shekarar 2025 na sama da naira biliyan 698 na ayyukan gwamnatin jihar da kuma naira biliyan 184 na ayyukan kananan hukumomi 27.

Hakan ya biyo bayan gabatarwa da kuma amincewa da rahoton zaunannen kwamitin kasafin kudi na majalisar.

Da yake gabatar da rahotan shugaban kwamitin wanda shi ne mamba mai wakiltar mazabar Malam Madori, Alhaji Hamza Adamu Ibrahim ya bayyana cewa dukkanin kwamitocin majalisar sun tantance tanade-tanaden kasafin kowace ma’aikatar da hukumar domin yin gyara ko kari a cikin kasafin kudin.

A cewarsa, kwamitocin sun kuma yi da masu ruwa da tsaki daban-daban da suka hada da kungiyoyin farar hula tare da gudanar da aikin tantancewa a kokarin da ake na isa ga wani cikakken daftarin kasafin kudi domin gabatar da shi ga zaman majalisar.

Bayan amincewar baki daya ta hanyar kada kuri’a, kakakin majalisar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya sanar da amincewa da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 ya zama doka.

  • Labarai masu alaka

    Gwamna Radda Ya Nada Sabuwa Kwamishinoni, Manyan Mataimaka na Musamman

    Da fatan za a raba

    Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda ya nada Alhaji Muhammad Sani Ali Ahmad da Alhaji Mannir Ayuba Sullubawa a matsayin kwamishinonin da majalisar dokokin jihar Katsina ta tabbatar.

    Kara karantawa

    Ramadan: Mutum 4 sun mutu sakamakon cinkoson ababen hawa saboda kyaututtuka.

    Da fatan za a raba

    Rundunar ‘yan sandan jihar katsina ta tabbatar da mutuwar mutane hudu a lokacin cinkoson ababen hawa don kyaututtukan Ramadan a gidan wani mai taimakon jama’a na katsina.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe
    Jawabin cikin layi
    Duba duk sharhi

    Labarai daga Jihohi

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki

    Gwamna Abdulrazaq ya yi Allah wadai da harin Eruku,

    Gwamna Abdulrazaq ya yi Allah wadai da harin Eruku,
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x