Gamayyar kungiyoyin farar hula sun roki gwamnatin Katsina da ta sa baki kan jinkirin EHR a cibiyoyin kiwon lafiya na jihar

Da fatan za a raba

Gamayyar kungiyoyin farar hula ta jihar Katsina tayi kira ga Gwamna Dikko Umar Radda kan ya duba yadda za’a inganta tsarin amfani da Internet wajen gudanar da aikace-aikacen kiwon lafiya a manyan asibitocin jihar Katsina.

Wannan na a cikin wata takarda ne mai dauke da Sa Hannun Shugaban Kungiyar Malam Abdul Rahman Abdullahi Dutsinma wanka aka aikoma Madubin Katsina.

A cewar wannan Takarda wannan ya biyo bayan ziyarar gani da ido da gamayyayar kungiyoyin ta kai a wasu asibitocin tare da ganin yadda marassa lafiya ke faman jira a asibitocin kafin su samu kulawa sakamakon tsaiko da akan samu wajen yin amfani da tsarin Internet domin duba lafiyarsu.

Duk da yake akwai amfani da yawa tattare da tsarin wanda kuma yasa dole a jinjina ma gwamnati kan kawo tsarin, Gamayyar kungiyoyin na shawarartar gwamnati da ta duba yadda zata inganta tsarin ta yadda za’a kara karfin Internet din da kuma duba yiwuwar maida tsarin ya yi aiki lokacin da network ya dauke da yadda aikin zai iya hawa idan network ya dawo.

Wannan zai taimaka wajen rage dogon jira da wahalhalun da marassa lafiya ke fuskanta a asibitocin.

  • Labarai masu alaka

    Jam’iyyar PDP ta Kwara ta Kira ga Gwamnatin Tarayya da ta Binciki Bidiyon da ke yawo a yanar gizo na ‘Yan fashi da makami da ake zargin suna da alaka da KWSG

    Da fatan za a raba

    Jam’iyyar PDP reshen jihar Kwara ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta binciki bidiyon da ke yawo a yanar gizo da ke zargin kama wadanda ake zargi a jihar Edo da makamai da ababen hawa mallakar karamar hukumar Ifelodun ta jihar Kwara.

    Kara karantawa

    NOA ta ƙaddamar da wayar da kan jama’a kan tsaro a yankunan kan iyakar Katsina

    Da fatan za a raba

    Hukumar wayar da kan jama’a ta jihar Katsina (NOA) ta fara wani gangamin wayar da kan jama’a kan tsaro a yankunan kan iyakar jihar da nufin wayar da kan jama’a kan laifukan da ke yawo a kan iyakokin jihar da kuma tattara su don ƙara wa ƙoƙarin gwamnati na kawo ƙarshen rashin tsaro a jihar da kuma ƙasar baki ɗaya.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe
    Jawabin cikin layi
    Duba duk sharhi

    Labarai daga Jihohi

    Gwamna Abdulrazaq ya yi Allah wadai da harin Eruku,

    Gwamna Abdulrazaq ya yi Allah wadai da harin Eruku,

    YAN QARSHE SHIDA SUKA FITO A GASAR KW-IRS TAX KLUBU 2025

    YAN QARSHE SHIDA SUKA FITO A GASAR KW-IRS TAX KLUBU 2025
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x