Litinin ne ranar Hutu ga Jama’a don bikin Eid-Ul-Mawlid – FG

Da fatan za a raba

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar litinin 16 ga watan Satumba 2024 a matsayin ranar hutu domin murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

Da yake sanar da hakan a madadin gwamnati, Ministan Harkokin Cikin Gida, Dokta Olubunmi Tunji-Ojo, ya taya al’ummar Musulmin Nijeriya da kuma kasashen waje murna, inda ya ce, “Ina taya al’ummar Musulmi na gida da kuma na kasashen waje murnar wannan rana.

Dokta Tunji-Ojo ya bukaci al’ummar Musulmi da dukkan ‘yan Najeriya da su rungumi “ruhun hakuri, sadaukarwa, da juriya”. Ya kuma yi kira gare su da su yi amfani da wannan lokaci wajen yi wa kasa addu’ar zaman lafiya da ci gaba.

Sanarwar ta ce, “Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 16 ga Satumba, 2024 a matsayin ranar hutu domin murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

“Ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, wanda ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya, ya taya al’ummar musulmin gida da na kasashen waje murnar wannan rana.

“Dr. Tunji-Ojo ya bukaci al’ummar Musulmi da kuma ‘yan Najeriya da su yi koyi da ruhin hakuri, sadaukarwa, da juriya.

“Yayin da yake taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar wannan rana, Ministan ya roke su da su yi amfani da damar da suka samu wajen yin addu’o’in samun dawwamammen zaman lafiya da kuma samar da daidaito a tsakanin al’umma.”

  • Labarai masu alaka

    Labarin Hotuna: Gwamna Radda Ya Halarci Daurin Auren ‘Ya’yan Minista Kyari

    Da fatan za a raba

    A yau, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya halarci bikin daurin auren ‘ya’yank Ministan Aikin Gona da Tsaron Abinci, Sanata Abubakar Kyari.

    Kara karantawa

    Dangantakar Katsina da Yankin Kudu maso Yamma tana da Tushe Mai Karfi a Tarihin Siyasar Najeriya — Gwamna Radda

    Da fatan za a raba

    Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa dangantakar da ke tsakanin Katsina da yankin Kudu maso Yamma tana da tushe mai karfi a tarihin siyasar Najeriya, inda ya tabbatar wa al’ummar Yarbawa mazauna jihar cewa za su ci gaba da samun goyon baya, da damar shiga harkokin jiha, da kuma kariyar gwamnati.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe

    Labarai daga Jihohi

    ‘Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi A Kan Iyakar Zamfara da Katsina Da Harsasai 800 AK-47 A Cikin Tankin Mai Na Babura

    ‘Yan Sanda Sun Kama Wanda Ake Zargi A Kan Iyakar Zamfara da Katsina Da Harsasai 800 AK-47 A Cikin Tankin Mai Na Babura

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki

    Hukumar Kwastam ta Najeriya ta ziyarci hukumomin tsaro na ‘yan’uwa mata domin inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin da kuma tsaron kan iyakoki
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x