Mai martaba Sarkin Katsina Alhaji Dr. Abdulmumini Kabir Usman ya yi kira da a zauna lafiya

Da fatan za a raba

Mai martaba Sarkin Katsina Alhaji Dr. Abdulmumini Kabir Usman ya bayyana zaman lafiya a matsayin ginshikin kowace al’umma.

Alhaji Abdulmumini Kabir ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadarsa kan zanga-zangar da wasu matasa suka shirya yi a kasar.

Sarkin ya sanar da mutanen yankinsa cewa wanzar da zaman lafiya a tsakanin al’umma zai kawo ci gaba.

Ya nuna damuwarsa da wadanda suka shirya gudanar da zanga-zangar wadda ba za ta magance matsalar da talakawa ke fuskanta ba.

Alhaji Dr. Abdulmumini Kabir, ya shawarci dukkan shugabanni a kowane mataki da su yiwa mabiyansu adalci.

Ya kuma yi kira ga al’ummar yankinsa da su ci gaba da yi wa Allah addu’a domin ya magance wahalhalun da suke ciki.

  • Labarai masu alaka

    An Bukaci Iyaye Mata Su Bada Muhimmanci Ga Duba Lafiyarsu A Kullum Domin Hana Yaɗuwar Cutar HIV Daga Uwa Zuwa Jariri

    Da fatan za a raba

    An ƙarfafa iyaye mata su riƙa ziyartar cibiyoyin lafiya mafi kusa akai-akai don sa ido kan yanayin lafiyarsu, musamman a lokacin daukar ciki.

    Kara karantawa

    Bikin Kasuwanci: Matasa Suna Shirya Makomar Yau

    Da fatan za a raba

    An yi kira ga kamfanoni masu zaman kansu na Jihar Katsina da su gano ra’ayoyi masu kyau, su ba da jagoranci ga matasa ‘yan kasuwa, da kuma zuba jari a harkokin kasuwanci da matasa ke jagoranta.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe
    Jawabin cikin layi
    Duba duk sharhi

    Labarai daga Jihohi

    Gwamna Abdulrazaq ya yi Allah wadai da harin Eruku,

    Gwamna Abdulrazaq ya yi Allah wadai da harin Eruku,

    YAN QARSHE SHIDA SUKA FITO A GASAR KW-IRS TAX KLUBU 2025

    YAN QARSHE SHIDA SUKA FITO A GASAR KW-IRS TAX KLUBU 2025
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x