Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya taya mai girma gwamnan jihar Cross River, Prince Bassey Edet Otu murnar cika shekaru 66 da haihuwa.
A cikin sakon taya murna Gwamna Radda ya bayyana Gwamna Otu. wanda aka fi sani da Sweet Prince a matsayin jagora mai tausayi, mai hangen nesa, kuma mai bin tafarkin dimokuradiyya na gaskiya wanda shugabancinsa ke ci gaba da samar da fata da ci gaba ga al’ummar jihar Kuros Riba da sauran su.
Gwamna Radda ya lura cewa tafiyar siyasa ta Prince Otu, tun daga zamansa na majalisar wakilai da ta dattawa zuwa aikin da yake na gwamna a halin yanzu, na nuni da tsananin kishin aiki, karfafawa da gudanar da mulki baki daya. Ya kuma yaba masa bisa gina dauwamammen gado na ci gaban bil’adama, karfafa matasa, da kuma ci gaban al’umma ta hanyoyi daban-daban da suka shafi rayuka marasa adadi.
Gwamnan ya ci gaba da yabawa Gwamna Otu bisa kyakkyawan jagoranci a cikin gidan jam’iyyar APC, inda natsuwar sa da gogewarsa da tawali’unsa suka ci gaba da karfafa hadin kai da kuma samar da ci gaba mai dorewa a yankin kudancin kasar nan da ma fadin kasar nan.
“A madadin gwamnati da mutanen jihar Katsina nagari, ina taya dan uwana kuma abokin aikina, Mai Girma, Prince Bassey Edet Otu, murnar cika shekaru 66 da haihuwa, jajircewar ku na yi wa gwamnati hidima, tausayin jama’a, da sadaukarwar da kuke yi wajen samar da shugabanci nagari, ya kasance abin koyi a Nijeriya a yau,” in ji Gwamna Radda.
Gwamna Radda ya yi addu’ar Allah ya kara wa Gwamnan Jihar Kuros Riba da karin shekaru masu yawa cikin koshin lafiya, da hikima, da kuma karfin gwiwa don ci gaba da yi wa al’ummarsa hidima da bayar da gudummawar ci gaban kasa.
Ya kara da cewa “Bari wannan sabon zamani ya kawo zaman lafiya, cikawa, da alherin Allah yayin da kuke ci gaba da jagoranci cikin gaskiya da tausayi,” in ji shi.
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
18 ga Oktoba, 2025



