
Uwargidan gwamnan jihar Katsina, Hajiya Zulaihat Dikko Radda, ta yi kira ga mata a fadin jihar da su ci gaba da marawa mijinta, Gwamna Malam Dikko Umar Radda baya, a kan kudirinsa na ciyar da jihar Katsina da Najeriya gaba gaba.
Ta bada tabbacin cewa za a gudanar da ayyukan raya kasa a cikin shekara da kuma shekaru masu zuwa domin inganta rayuwar al’ummar jihar.
Hajiya Zulaihat ta bayyana haka ne a yayin kaddamar da wani littafi mai taken “Aikin Sauyi na Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda da Mai dakinsa Hajiya Zulaihat Dikko Radda” wanda aka gudanar a dakin taro na Hukumar da ke Katsina.
Hakazalika Gwamna Malam Dikko Umar Radda ya sayi kwafin littafin a kan kudi Naira miliyan biyu, yayin da matarsa Hajiya Zulaihat Dikko Radda ita ma ta sayi kwafin daya kan Naira miliyan 1.
A jawabinta na maraba, shugabar kwamitin shirya taron Hajiya Amina Adamu Dan’iyau ta yi maraba da dukkan baki tare da bayyana fatan sauran jahohin jihar Katsina za su yi koyi da irin jagoranci nagari da kuma jajircewar ci gaba a jihar Katsina.
A nasu jawabin shugaban karamar hukumar Baure, Alhaji Yusuf Macheka wanda ya wakilci shugaban karamar hukumar Alhaji Sani Suleiman da Hajiya Talatu Nasir sun yabawa marubucin bisa rubuta nasarorin da gwamnan da uwargidansa suka samu.
A jawabinta na godiya, marubuciyar littafin, Hajiya Hassana Aliyu, ta bayyana jin dadin ta bisa gagarumin goyon bayan da aka samu a yayin kaddamarwar.



