







Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, a yau ya bi sahun sauran Gwamnoni wajen tarbar mai girma shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, a lokacin da ya sauka a filin jirgin sama na Sam Mbakwe, Owerri, jihar Imo.
Shugaba Tinubu ya je jihar ne domin kaddamar da wasu muhimman ayyuka na gado da Gwamna Hope Uzodinma ya aiwatar. Ayyukan da aka shirya kaddamar da su sun hada da Otal din Imo Concorde Hilton, da Emmanuel Iwuanyanwu International Conference Centre, Asumpta Flyover, da Cibiyar Koyon Dijital ta Imo.
Gwamna Uzodinma ne ya tarbi shugaban kasar tare da wasu gwamnonin Najeriya karkashin jagorancin shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya, AbdulRahman AbdulRazaq na jihar Kwara. Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Gwamna Mai Mala Buni na Yobe, Gwamna Ahmed Namadi na Jigawa, Gwamna Abdullahi Sule na Nasarawa, Gwamna Babajide Sanwo-Olu na Legas, Gwamna Ahmed Aliyu na Sakkwato, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na Gombe, Gwamna Uba Sani na Kaduna, da sauran su.
Haka kuma akwai Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, tare da wasu manyan jami’an gwamnati.