
Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Umar Faruq Umar ya bukaci wadanda suka cancanta a jihar Katsina da su fito kwansu da kwarkwatansu wajen gudanar da rijistar masu kada kuri’a a fadin kasa baki daya.
Alhaji Umar Faruq Umar ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya karbi bakuncin sabbin zababbun shugabannin kungiyar Arewa Consultative Forum reshen jihar Katsina karkashin jagorancin shugaban kungiyar Alhaji Shehu Musa Malumfashi a ziyarar ban girma da suka kai masa.
Mai martaba Sarkin Daura Alhaji Umar Faruq Umar ya ce kiran ya zama wajibi matuka domin ta hanyar karbar katin zabe ne kawai mutanen da suka cancanta su yi amfani da ‘yancinsu na kasa a lokacin zabe.
Alhaji Umar Faruq Umar ya yi nuni da cewa kungiyar tuntuba ta Arewa reshen jihar na da muhimmiyar rawa wajen wayar da kan jama’a kan tasirin aikin wanda na daya daga cikin manyan batutuwan da suka shafi kasa baki daya.
Sarkin ya bayyana jin dadinsa kan yadda aka kafa dandalin a jihar Katsina domin baiwa ‘ya’yan kungiyar damar bayar da gudunmuwarsu wajen magance matsalolin da suka addabi al’ummar jihar da ma Arewacin Najeriya baki daya.
Ya kuma bukaci sabbin zababbun shugabannin kungiyar da su yi aiki tukuru wajen samar da zaman lafiya, hadin kai da fahimtar juna a tsakanin jama’a domin ci gaban jihar Katsina da jihohin Arewa baki daya.
Sarkin Daura ya ba da tabbacin cewa Masarautar za ta bai wa dandalin duk wani goyon bayan da ya dace domin cimma burin da aka sanya a gaba.
Shugaban kungiyar Arewa Consultative Forum reshen jihar Katsina Alhaji Shehu Musa Malumfashi ya ce sun kasance a fadar mai martaba sarki ne domin gabatar da kansu a matsayin zababben shugabanni da kuma neman shawararsa ta uba.
Alhaji Shehu Musa Malumfashi ya bayyana cewa an kafa kungiyar Arewa Consultative Forum ta jihar ne a shekarar 2024 tare da shugabanni masu rike da madafun iko kuma wasu watanni baya aka zabe su a matsayin sabbin shugabannin kungiyar.
Ya bayyana cewa kungiyar ta gudanar da wasu ayyukan jin kai da suka hada da daukar nauyin wasu yara kan aikin tiyatar zazzabin typhoid a asibitin koyarwa na gwamnatin tarayya Katsina, da samar da magunguna da za a rabawa cibiyoyin kiwon lafiya da kara wayar da kan al’umma kan illar rajistar masu kada kuri’a ta hanyar damfara da sauransu.
Ya nemi goyon bayan sarki da hadin kai domin samun nasarar da ake bukata.
Tun da farko, Sakataren yada labarai na kungiyar Alhaji Sada Salisu Rumah wanda kuma Danwairen Katsina ya yi tsokaci sosai kan dalilan kafa kungiyar reshen jihar da kuma irin yadda mutanen da abin ya shafa suka hada da dattijai, masu rike da mukaman gargajiya, da mutane daban-daban masu kima a fadin jihar.
Alhaji Sada Salisu Rumah ya bada tabbacin cewa shugabannin kungiyar za su yi aiki tukuru domin ci gaban jihar Katsina baki daya da Arewacin Najeriya baki daya.


