
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda a yau ya karbi bakuncin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a ziyarar ta’aziyya da ya kai wa uwargidan tsohon shugaban kasa, Hajiya Aisha Muhammadu Buhari a gidan marigayi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da ke Kaduna.













Shugaba Tinubu ya samu kyakkyawar tarba daga Gwamna Radda, Yusuf Buhari, da sauran iyalan marigayin.
Ziyarar ta zo ne jim kadan bayan da shugaban ya halarci daurin auren Fatiha Nasiruddeen Abdulaziz Yari, dan tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma Sanata Abdulaziz Yari, wanda aka gudanar a masallacin Sultan Bello Kaduna.
An yi addu’o’i na musamman ga Allah ya jikan marigayi shugaban kasa Muhammadu Buhari, tare da rokon Allah Madaukakin Sarki da ya gafarta masa kurakuransa, ya kuma ba shi Aljannatul Firdaus ta zama masaukinsa na karshe.
An kuma yi addu’o’i ga masoyiyar uwargidan sa, Hajiya A’isha Buhari, da ‘ya’yansa, da sauran iyalansa baki daya, tare da rokon Allah Ya ba su lafiya da kwanciyar hankali. An kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su kiyaye kimar kishin kasa, rikon amana da hidima da ake girmama marigayin.
A nasa jawabin, shugaba Tinubu ya jaddada kudirinsa na gina ginshiki mai kyau da kuma abubuwan da marigayi shugaban kasa ya bari a baya, inda ya ce rayuwar Buhari da hidimar kasa za ta ci gaba da zaburar da al’umma.
Shugaban ya samu rakiyar manyan jami’an gwamnati da suka hada da gwamnan jihar Kaduna Sanata Uba Sani; Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio; Kakakin majalisar wakilai Rt. Hon. Tajudeen Abbas; Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin; Sanata Abdulaziz Yari; tsohon Gwamna Isa Yuguda na Bauchi da Simon Lalong na Filato; haka kuma da dama daga cikin ministoci da sanatoci da manyan hadiman shugaban kasa, ciki har da Alhaji Ibrahim Kabir Masari, mai ba shi shawara na musamman kan harkokin siyasa.
Wadanda suka halarci taron sun hada da makusantan marigayi shugaban kasar da suka hada da Alhaji Musa Haro da Danmadamin Daura da Hakimin Durmukol da sauran ‘yan uwa na gidan Buhari.