
Uwargidan gwamnan jihar Katsina Hajiya Zulaihat Dikko Radda ta bukaci iyaye mata masu shayarwa da su shayar da ‘ya’yansu nonon uwa zalla na tsawon watanni shida.
Hajiya Zulaihat ta yi wannan kiran ne a yayin taron makon shayarwa da nonon uwa na duniya na shekarar 2025 da aka gudanar a dakin taro, ofishin First Lady of Government House Katsina.
Ta kuma jaddada bukatar shayar da jarirai nonon uwa zalla, sannan ta yi kira ga jakadun tawagar likitocin da dukkan shugabannin kananan hukumomi 34 da su fara tun daga tushe, kofa gida kan yadda za su rika shayar da mata masu shayarwa a gidansu.
A nasa jawabin kwamishinan lafiya Dr Musa Adamu Funtua ya yaba da wannan karimcin tare da yin alkawarin gwamnati ta kudiri aniyar tallafawa kokarin da ake na tabbatar da shayar da jarirai nonon uwa zalla.
A jawabansu daban daban babban sakataren hukumar kula da kiwon lafiya matakin farko Dr Shamsudeen Yahaya da Mrs Roda da Dr Umar Bello sun yi magana sosai kan muhimmancin shayarwa.
Babban abin da ya fi daukar hankali a taron shi ne rabon buhunan shinkafa, Milet, Masara, pampers, da tsabar kudi naira dubu dari ga kowace mace guda uku da aka zabo daga kananan hukumomi daban-daban.
Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin ta godewa kokarin Gwamnati na tallafawa mata masu shayarwa guda uku a jihar.


