
Wani kazamin bindiga da ya barke tsakanin jami’an tsaro da ‘yan bindiga a karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina ya yi sanadiyar mutuwar ‘yan sanda uku da farar hula guda.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Abubakar Aliyu ya tabbatar da faruwar lamarin.
An samu labarin cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari a kauyuka uku na Kadisau, Raudama da Sabon Layi, da ke cikin karamar hukumar Faskari a yammacin ranar Talata.
A cewarsa, jami’an tsaro da suka hada da ‘yan sanda da na rundunar sojojin sama na Najeriya suka yi gaggawar tunkarar ‘yan bindigar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan ya bayyana cewa “A ranar 8 ga watan Yuli, 2025, da misalin karfe 1700, wani rahoto kan harin da ‘yan bindiga suka kai kauyuka uku (3) na Kadisau, Raudama, da Sabon Layi, a karamar hukumar Faskari, jihar Katsina, inda suka yi yunkurin yin garkuwa da mazauna garin tare da yin awon gaba da dabbobi.
“Bayan samun rahoton, ba tare da bata lokaci ba, DPO ya tattara tare da mayar da martani tare da taimakon Dandume da rundunar sojojin saman Najeriya (NAF) 213 FOB, Air Component.
“Da isowar tawagar ‘yan sandan sun yi artabu da ‘yan ta’addan a wani mumunar bindiga, wanda ya yi sanadin kashe ‘yan bindiga da dama, wasu kuma sun jikkata.
“Abin takaici, wasu jaruman ‘yan sanda uku (3) sun rasa rayukansu a bakin aiki da wani farar hula.
“Kwamishanan ‘yan sandan jihar Katsina, CP Bello Shehu, psc, fdc, MNIM, yayin da yake yabawa wannan bajinta da sadaukarwar da jami’an suka yi, ya yi addu’ar Allah ya jikan jami’an da suka rasu.
“Ya kuma kara ba jama’a tabbacin ci gaba da kokarin hukumar na tabbatar da tsaro da tsaron al’ummar jihar inda ya yi kira ga mazauna jihar da su sanya ido tare da kai rahoto ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa.