
An bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya tabbatar da sa ido sosai kan yadda aka fitar da kudade naira biliyan 758 domin warware duk wasu basussukan fensho da ake bin su domin hana yin zagon kasa.
A wata sanarwa da kungiyar Muslim Media Watch Group ta Najeriya, kodineta na kasa, Alhaji Ibrahim Abdullahi ya fitar, ya kuma yabawa shugaba Tinubu kan matakin da ya dauka na rage wa ‘yan fansho na tarayya daga halin kuncin da suke ciki.
A cewar sanarwar, dole ne a sanya ido sosai kan sabuwar manufar domin hana duk wani zagon kasa daga wasu Ma’aikatan Asusun Fansho (PFA) da ake zargi da batawa wasu ‘yan fansho da suka yi rajista da su rai.
Ya bayyana cewa wasu Ma’aikatan Asusun Fansho sun kara wa ‘yan fansho matsalolin da suke fuskanta ta hanyar jinkirta biyan su fansho kusan shekaru 2 bayan sun yi ritaya.
Ta ce duk irin wadannan laifuffuka da rashin iya aiki sun karfafa cin hanci da rashawa a sassan al’umma na tattalin arzikin kasa.
Sanarwar ta yi kira da a samar da cikakken tsari da ingantaccen tsarin sa ido daga fadar shugaban kasa da hukumar fansho ta kasa PENCOM wajen magance matsalolin ‘yan fansho gaba daya.
Tana kira ga Gwamnonin Jihohi a fadin Tarayya da su yi koyi da Gwamnatin Tarayya wajen biyan basussukan da ake bin Jihohi da Kananan Hukumomi.
Sanarwar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta yin la’akari da gyaran dokokin da suka dace don hukunta laifukan tattalin arziki da ake tafkawa a Najeriya.