
Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ce ta fara gudanar da bincike kan kisan Alhaji Idris Abubakar, shugaban kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) na jihar.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Adetoun Ejire-Adeyemi ya fitar, ya ce an harbe shugaban ne a ranar 8 ga Maris, 2025 a kofar gidansa da ke Oke-Ose, a unguwar Ilorin.
A cewar sanarwar, jami’an ‘yan sanda sun mayar da martani cikin gaggawa tare da gano harsashi 7.62mm da aka kashe a wurin da lamarin ya faru.
Ya yi bayanin cewa Hukumar Binciken Laifukan Jiha (SCID) ta fara gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
Ta kuma bada tabbacin za a gurfanar da wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya, sannan ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da bayanai masu amfani ga ‘yan sanda.
A halin da ake ciki kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria reshen jihar Kwara, ta bayyana kaduwarta dangane da kisan da aka yi wa shugaban kungiyar Alhaji Idris Abubakar Sakaina, wanda wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kashe a jiya a wani mazaunin gidansa da ke Oke-ose da misalin karfe 10 na dare.
A wata sanarwa da shugaban Fulanin (Ardon Ardodi) a jihar Kwara, Alhaji Ojonla Mahmud ya fitar dauke da sa hannun sakataren kungiyar MACBAN na jihar, AbdulAzeez Muhammed ya bukaci hukumomin tsaro da su gaggauta zakulo wadanda suka gudu domin tabbatar da sun fuskanci hukunci.
Sanarwar ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta taimaka wa iyalan mamacin wajen samar da ingantaccen ilimi ga yaran da kuma kyautata jin dadin su.
Ya ce an binne gawar marigayin a zango da ke Ilorin. KARSHE
REL/ALI MUHAMMAD RABIU