Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana matukar bakin ciki game da rasuwar Alhaji Nasiru Mohammed Tsauri, Shugaban Kungiyar Kwankwasiyya a Jihar Katsina kuma Mataimakin Shugaban Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party.
Gwamna Radda ya bayyana marigayi Alhaji Tsauri a matsayin gwarzon siyasa wanda rasuwarsa babban rashi ne ga Jihar Katsina.
“Alhaji Nasiru Mohammed Tsauri mutum ne mai gaskiya da rikon amana. Abokin siyasa ne, duk da cewa mun fito daga tushe daban-daban na akida. Gaskiyarsa da jajircewarsa ga hidima ba za a iya musantawa ba,” in ji Gwamnan.
Ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa marigayin, Ya ba shi Al-Jannah Firdaus, Ya kuma ba iyalansa ƙarfin jure rashin da ba za a iya gyarawa ba.
Gwamna Radda ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai, Kungiyar Kwankwasiyya, NNPP, da kuma al’ummar Karamar Hukumar Kurfi.
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
9 ga Fabrairu, 2026



