
Jihar Katsina ta samu gagarumin ci gaba a fannin tattalin arziki, ta hanyar tattara babban abin da ya samu a cikin gida na tsawon shekaru biyar a jere, wanda ya hada da 2019 zuwa 2023, tare da tallafin bankin duniya.
Babban jami’in kididdiga na jihar, Farfesa Saifullahi Sani Ibrahim ne ya sanar da hakan a yayin wani taron karawa juna sani na tsawon kwanaki biyar akan GDP da CPI, wanda aka fara a ranar 24 ga watan Satumba wanda za a kammala ranar 28 ga Satumba, 2025.
Nasarar mai dimbin tarihi ta sanya Katsina a matsayin jagaba wajen tattara bayanan tattalin arziki a tsakanin jihohin Najeriya.
Farfesa Ibrahim ya bayyana cewa ma’aikatan ofishin kididdiga na jihar Katsina sun shiga cikin dukkanin matakai da suka hada da tattara firam, tattara bayanai, da nazari.
“Tare da lambobin GDP, yanzu jihar za ta iya samar da tsare-tsaren tattalin arziki da za a iya aiwatar da su kamar shirin raya Jiha, Tsarin kashe kudi na matsakaicin wa’adi da dabarun sashe na matsakaici,” in ji shi.
Babban jami’in kididdigan ya bayyana cewa alkaluman GDPn sun nuna yadda jihar ke habaka tattalin arzikinta a fannonin noma, masana’antu, da zamantakewa, wanda hakan ke nuna ra’ayin Gwamna Dikko Radda na sanya jihar Katsina cikin manyan kasashen da ke kan gaba a tattalin arzikin Najeriya.
Hakazalika, Farfesa Ibrahim ya bayyana cewa Gwamna Radda ya amince da tattara bayanan GDP na shekarar 2024 da 2025, wanda hakan ya sa Katsina ta zama jiha ta farko a Najeriya da ta fara inganta GDP na lokaci-lokaci.
Da yake mayar da martani ga wannan ci gaban, bankin duniya ya tura tawagar kwararru don karfafa karfin masana tattalin arziki da kididdiga wadanda za su tattara GDP na 2024-2025 da lissafin CPI na wata-wata. Bankin Duniya ya kara yabawa Gwamna Radda bisa inganta tsarin kididdiga na Jihohi da kuma sanya ta zama wuri na farko na ziyarar karatu da sauran jahohin suka yi.
Farfesa Ibrahim ya bayyana nasarar da aka samu a matsayin muhimmin mataki na samar da manufofi masu tushe da kuma tsare-tsare na tattalin arziki a jihar.