
Babban Daraktan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Katsina, Alhaji Yunusa Abdullahi Dankama, ya gudanar da taro a yau tare da daraktocinsa, da shugaban hukumar, da sauran mambobin hukumar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Alhaji Badaru Bello Karofi ya sanyawa hannu kuma ya mika wa dakinmu na labarai.
Sanarwar ta ce taron na daga cikin shirye-shiryen gudanar da aikin Hajji mai zuwa.
A jawabinsa na maraba a wajen taron, Shugaban Hukumar Alhaji Kabir Bature Sarkin Alhazai wanda daya daga cikin ‘yan kwamitin Alhaji Ahmed Aliyu Radda ya wakilta ya yi musu fatan alheri, ya kuma bukace su da su hada kai domin samun nasara a aikin Hajjin da ke tafe, kamar yadda suka yi a bara.
Da yake karin haske ga mambobin hukumar kan shirye-shiryen da hukumar ta yi da kuma ci gaban da aka samu kawo yanzu, Alhaji Yunusa Abdullahi Dankama, ya yi cikakken bayani kan rajistar maniyyata da karbar kudin aikin Hajjin bana.
Ya bayyana cewa hukumar ta karbi kason kudin aikin Hajji guda 3,680 daga hukumar alhazai ta kasa, kuma a halin yanzu an yiwa alhazai kimanin 1,850 rajista wadanda suka biya kudin aikin Hajjin.
Babban Daraktan ya kuma sanar da mambobin hukumar sakamakon taron da hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) ta kira a makon jiya wanda ya mayar da hankali musamman kan jigilar jirage, hukumar alhazai ta Najeriya ta amince da kamfanin jirgin Max Air da ke da iyaka da jigilar alhazai daga jihar Katsina.
Dangane da batun jigilar jirage, ya ce alhazan jihar Katsina ne za su kasance rukuni na karshe da za a kai kasar Saudiyya.
Alhaji Yunusa Dankama ya mika godiyarsa ga Gwamna Mallam Dikko Umar Radda PhD bisa goyon baya da hadin kai da yake bayarwa wajen ganin an samu nasarar ayyukan hukumar.