Kungiyar Cigaban Al’umma ta Masarautar Daddara ta karrama wasu muhimman mutane da suka cancanta ‘ya’yan masarautar.
A ranar Laraba 01-01-2025 kungiyar ta karrama wasu daga cikin manyan mutane masu bada gudumawa da taimakon al’umma a masarautu da karamar hukumar Jibia a dakin taro na ma’aikatar karamar hukumar Katsina.
Da yake gabatar da jawabinsa, Hon. Halilu Buhari Kanwa, ya ce mun shirya wannan taron ne domin karrama wasu muhimman mutane da suka bayar da gudunmawar ci gaban al’umma ta fannoni da dama kamar ilimi, taimakon marasa lafiya, samar da ayyukan yi ga matasa, samar da ruwan sha da dai sauransu.
Shugaban kungiyar ya yabawa gwamnan jihar Katsina bisa kokarinsa na inganta rayuwar al’ummar jihar Katsina.
A nasa jawabin shugaban karamar hukumar Jibia wanda ya samu wakilcin sakataren karamar hukumar ya yabawa kungiyar bisa karrama wadannan mutane da kowa ya san irin gudunmawar da suke bayarwa a masarautar Daddara da karamar hukumar Jibia baki daya.
Wadanda aka karrama sun hada da Hon. Shafi’u Abdullahi, Direct of Library Board in Katsina state, Alh Lawal Sulaiman, Alh Abdullahi Riko, Alh Ibrahim Isah, Dr. Lawal Ishye, da dai sauransu.
Da yake gabatar da jawabinsa a madadin wadanda aka karrama, Daraktan Hukumar Laburare ta Jihar Katsina, Hon. Shafiu Abdullahi, ya godewa Allah da ya yi masa, ya kuma yabawa kungiyar bisa kokarin da take yi na kawo ci gaba a yankinsu.
Taron ya samu halartar wakilin shugaban ma’aikatan gwamnatin jihar Katsina Hakimin Daddara Alh. Usman Usman Nagogo, Shugaban Kaita Yazeed Abdulkarim, ‘yan uwa da abokan arziki.



