Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Jihar Katsina Alh. Bala Abu Musawa Ya Jagoranci Mika Tutar Takara Ga Ƴan Takarar Kansilolin Mazaɓu Goma Na Ƙaramar Hukumar Jibiya

Da fatan za a raba

A ranar Laraba 29/1/2025 mataimakin shugaban jam’iyyar APC na jihar Katsina Alh. Bala Abu Musawa, tare da Ɗan takarar shugabancin ƙaramar hukumar Jibia Hon. Surajo Ado, suka jagoranci miƙa tutar takarar ga ƴan takarar Kansilolin mazaɓu goma na ƙaramar hukumar ta Jibia.

Bayan kammala miƙa tutocin, mataimakin shugaban jami’iyyar APCn na jiha Alh. Bala Abu Musawa, ya gabatar da jawabin shi a wurin taron, inda ya fara da nuna farin cikin sa da Allah SWT ya nuna mashi wannan rana mai matuƙar muhimmanci wacce za’a miƙa wannan tutoci ga yan takarar ƙaramar hukumar da ma wasu ƙananan hukumomin kamar yadda uwar jam’iyyar ta jiha ta umarta

Ya cigaba da cewa” na baro ƙaramar hukumar ta musawa na taho Jibia mussaman saboda miƙa wannan tutoci ga ƴan takarar wannan ƙaramar hukuma domin aminci da ke tsakani na da al’ummar ƙaramar hukumar Jibia.

Dan gane da Ɗan takarar shugaban ƙaramar hukumar kuma Hon. Surajo Ado, nasan mutumin kirki ne sabo da ina da tabbacin ƙaramar hukumar Jibia tana daga cikin ƙananan hukumomin da suka dace Ɗan takara, sabo da munyi aiki tare lokacin da yake shugaban jam’iyyar wannan ƙaramar hukumar.

Ina da tabbacin Hon. Surajo Ado, ba zai bada kunya ba, an fiddo mutumin kirki wanda zai ciyar da ƙaramar hukumar Jibia gaba.

Shima a nashi jawabin, Ɗan takarar shugaban Hon. Surajo Ado, ya yi godiya ga al’ummar ƙaramar hukumar Jibia akan ƙauna da soyayya da suke nuna mashi, inda ya basu tabbacin gudanar da shugabanci na adalci wanda kuma zaiyi ƙoƙarin kawo abubuwan cigaba a ƙaramar hukumar.

Tun da fari da yake bayyana maƙasudin taron shugaban Jami’iyyar APC na ƙaramar hukumar Jibia Hon. Nasiru Al’mustapha Danye, ya bayyana cewa kamar yadda uwar jam’iyyar ta jiha ta bada umarni na ƙaddamar da wannan taro a kowace karamar hukuma, mu ma yau mun taru ne domin miƙa wannan tuta ga yan takarkarun mu na kansiloli domin basu damar fara gudanar da yaƙin neman zaɓe.

Mutane da dama ne su ka tofa albarkacin bakinsu yayin taron gangamin bada tutar ga ƴan takarar kansilolin.

Daga ƙarshe kamar yadda ya saba jagoran jam’iyyar ta APC ya karɓi wasu ‘ƴaƴan jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC, sabo da gamsuwa da suka yi da salon mulkin gwamnan jihar katsina Malan Dikko Umar Radda PhD.

Taron bada tutar ya samu halar manyan masu ruwa da tsaki na ƙaramar hukumar, ƴan uwa da kuma abokan arziki.

  • Labarai masu alaka

    KUFC ta zabi yan wasa daga KFA gabanin NPFL 2025/2026 mai zuwa.

    Da fatan za a raba

    Katsina Football Academy ta taya ‘yan wasanta biyar murna da kungiyar kwallon kafa ta Katsina United ta zabo gabanin gasar NPFL 2025/2026 mai zuwa.

    Kara karantawa

    Iyalan tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ne suka sanar da rasuwarsa.

    Da fatan za a raba

    Labarin ya tabbatar da shi a cikin wata sanarwa da Bashir Ahmed, tsohon mataimakin kafofin watsa labaru na Buhari, kuma Garba Shehu, mataimaka ne na musamman ga kafofin watsa labarai.

    Kara karantawa

    0 0 kuri'u
    Ƙimar Labari
    Subscribe
    Sanar da
    guest

    0 Sharhi
    Mafi tsufa
    Sabuwa Mafi Yawan Zabe
    Jawabin cikin layi
    Duba duk sharhi

    Labarai daga Jihohi

    KW-IRS Ya Kammala Gasar Tambayoyi Tax Club 2025 Matakan Farko

    KW-IRS Ya Kammala Gasar Tambayoyi Tax Club 2025 Matakan Farko

    Hukumar NDLEA ta kama kilo 1.8 na miyagun kwayoyi tare da kama mutane 1,025 da ake zargi a jihar Kwara.

    Hukumar NDLEA ta kama kilo 1.8 na miyagun kwayoyi tare da kama mutane 1,025 da ake zargi a jihar Kwara.
    0
    Bayyana tunanin ku kuma sami bayanai kyautax
    ()
    x