A safiyar ranar Asabar, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya karbi bakuncin tsohon dan Majalisar Wakilai ta Tarayya, Hon. Abdulaziz Ahmed Tijjani Bega, tare da magoya bayansa a birnin Kano.
Wannan ziyarar ta bai wa Gwamnan da tawagar tasa damar musayar ra’ayoyi kan yanayin siyasa na yanzu da kuma batutuwan da suka shafi ci gaban Jihar Katsina baki daya.
Gwamna Radda ya yi maraba da tsohon dan majalisar da magoya bayansa, inda ya jaddada muhimmancin ci gaba da tattaunawa a tsakanin masu ruwa da tsaki a harkar siyasa, tare da sanya muradun jihar a gaba fiye da bukatun kansu.
Ya bayyana cewa hadin kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyya yana da matukar muhimmanci wajen gina tsarin siyasa mai karfi da zai iya tallafawa manufofin ci gaban jihar.
Haka kuma, Gwamnan ya karfafa gwiwar ci gaba da hadin gwiwa a tsakanin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC, inda ya nuna kwarin gwiwar cewa fahimtar juna da hadin kai za su karfafa jam’iyyar yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen babban zaben shekarar 2027.
A baya, Hon. Bega ya wakilci mazabar tarayya ta Funtua/Dandume a Majalisar Wakilai tsakanin shekarar 2007 da 2011.
Taron ya samu halartar mamba a hukumar raya yankin Arewa maso Yamma (Northwest Development Commission), Hon. Shamsu Sule Funtua, da kuma Shugaban Kamfanin A.A. Albasu Nigeria Limited, Alhaji Abdullahi Abubakar Albasu.


















