- Ya Ci Karo da Jerin Gwano na Maulidi
A ranar Asabar, yayin da yake dawowa daga Kano zuwa Katsina, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya tsaya a garin Kazaure na Jihar Jigawa, inda ya ci karo da jerin gwano na bikin Maulidi.
Gwamnan ya tsaya na ɗan lokaci domin gaisawa da mahalarta taron tare da yi musu fatan alheri yayin da suke gudanar da bikin Maulidin.
A nasu bangaren, mahalarta taron sun yi wa Gwamnan addu’o’i tare da bayyana fatan samun zaman lafiya, nasara, da ci gaba a kokarinsa na bunkasa Jihar Katsina.
Gwamna Radda ya nuna godiyarsa kan karamcin da aka nuna masa da kuma addu’o’in da aka yi masa, sannan ya yi wa al’ummar fatan ci gaba da samun zaman lafiya, wadata, da albarkar Allah.












