Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya nuna matuƙar baƙin ciki tare da miƙa ta’aziyyarsa ga tsohuwar Kwamishinar Harkokin Mata, Hajiya Hadiza Abubakar Yar’adua, bisa rasuwar ɗanta na fari, Abubakar Usman Tuggar.
Abubakar Usman Tuggar, mai shekaru 18, ya rasu a ranar Talata, 4 ga Agusta, 2026, bayan ɗan gajeren rashin lafiya. Ya kammala karatunsa na sakandare kwanan nan a Burtaniya, an yi masa jana’iza a Makabartar Gudu, Abuja, bayan sallar Janazah a Masallacin Ƙasa.
Gwamna Radda ya bayyana mutuwar matashin Abubakar a matsayin babban rashi mai raɗaɗi, yana mai cewa rasuwar yaro yana ɗaya daga cikin manyan jarabawa a rayuwa.
“Mutuwar wani matashi mai albarka a irin wannan ƙaramar shekaru abin tausayi ne. Duk da cewa babu wata kalma da za ta iya rage radadin rashin ɗa da ake ƙauna,” in ji Gwamnan.
Ya yi addu’ar Allah (SWT) ya gafarta wa mamacin kurakuransa, ya shigar da shi Aljannatul Firdaus, ya kuma ta’azantar da Hajiya Hadiza Abubakar Yar’adua, dukkan iyalai, da duk masoya a wannan mawuyacin lokaci.
“A madadin Gwamnati da mutanen Jihar Katsina nagari, ina mika ta’aziyyarmu ga Hajiya Hadiza Abubakar Yar’adua da iyalanta. Allah (SWT) Ya gafarta wa mamacin, Ya ba shi Aljannatul Firdaus, Ya kuma ba iyalan karfin jure wannan rashin,” Gwamna Radda ya yi addu’a.
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
5 ga Agusta, 2026



