Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya jajantawa al’ummar garin Dangamau da ke karamar hukumar Kusada sakamakon guguwar iska da ruwan sama da ya lalata gidaje da ababen more rayuwa a cikin makon.
Gwamna Radda ya bayyana lamarin da ya raba gidaje da shaguna da kadarorin da bai wuce 200 da muhallansu a matsayin mai raɗaɗi da bakin ciki ba, inda ya ce asarar matsuguni da kadarori ya jawo wa iyalai wahala a cikin al’umma.
“A madadin gwamnati da mutanen kirki na jihar Katsina, ina jajantawa wadanda wannan bala’i ya rutsa da su a Dangamau, muna jin zafin ku kuma ba za mu bar ku ku kadai ba a halin yanzu.” Inji Gwamnan.
Gwamnan ya umurci hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta yin bincike tare da tantance irin barnar da aka yi. Ya kuma tabbatar da cewa tuni gwamnatin jihar ta dukufa wajen samar da kayan agaji cikin gaggawa da kuma tallafi ga gidajen da abin ya shafa.
Ya kara da cewa, “ana kokarin kawo tallafi ga ‘yan gudun hijirar.
Gwamna Radda ya kuma bukaci mazauna yankin da su kwantar da hankula tare da bayar da hadin kai ga kungiyoyin agajin da ke kasa a yayin da gwamnati ke kokarin dawo da zaman lafiya a yankin.
Ya yi addu’ar Allah ya jikan dukkan mazauna garin, kuma Allah ya kiyaye faruwar irin wannan lamari.
Ibrahim Kaula Mohammed
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Katsina
26 ga Yuli, 2026



