Shugaban Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Katsina, Dr. Bishir Gambo Saulawa, ya bayyana goyon bayan da aka samu daga membobin jam’iyyar a matakin unguwanni da kananan hukumomi a matsayin babban abin da ya haifar da ci gaban jam’iyyar da kuma nasararta a zabuka.
Dr. Saulawa ya yi wannan furucin ne a lokacin rangadin godiya da ya kai kananan Hukumomin Sandamu, Baure, Zango, da Mai’adua domin hada kan ‘yan jam’iyyar da kuma magance korafe-korafen da aka samu daga zaben fidda gwani da aka gudanar kwanan nan.
Ya yi kira ga wadanda suka sha kaye a zaben fidda gwani da su dauki kayen da suka sha da zuciya daya su hada kai da jam’iyyar domin tabbatar da nasararta a babban zaben da za a yi a shekara mai zuwa.
Dr. Bishir Gambo ya ce ziyarar an kuma yi ta ne domin yaba wa jami’an jam’iyyar a matakin kananan hukumomi saboda goyon bayansu da jajircewarsu, tare da ba su damar yin abubuwan da za su taimaka wa ci gaban jam’iyyar a jihar.
A cewarsa, rangadin ya kuma samar da wata hanya ta mu’amala da jami’an APC don tattauna ayyukan jam’iyya da kuma tsara dabarun ƙarfafa jam’iyyar kafin babban zaɓen da ke tafe.
A dukkan yankunan kananan hukumomi da aka ziyarta, shugabannin kansilolin sun nuna farin cikinsu game da ziyarar da membobin zartarwa na jam’iyyar APC na jihar suka kai musu, suna bayyana hakan a matsayin wata alama ta nuna damuwar shugabannin da kuma jajircewarsu ga walwalar ‘yan jam’iyyar a matakin farko.
Shugabannin kansilolin sun kuma yaba wa Gwamna Dikko Umar Radda saboda aiwatar da ayyuka da dama da suka shafi mutane da ci gaba a yankunan kananan hukumominsu.
Sauran masu jawabi a tarurrukan sun haɗa da shugabannin ƙananan hukumomi na APC da shugabannin kwamitocin masu ruwa da tsaki daga yankunan ƙananan hukumomi da aka ziyarta.



