Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana cewa tsohon kakakin rundunar sojin Najeriya, Manjo Janar Rabe Abubakar, ya mutu ne a hannun ‘yan fashi duk da kokarin da gwamnati da hukumomin tsaro suka yi don tabbatar da an sako shi lafiya.
A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Tsaro, Dr. Nasiru Mu’azu ya fitar, gwamnati ta ce marigayi Manjo Janar ya mutu ne sakamakon matsalolin lafiya, ciki har da ciwon suga da hawan jini.
Gwamna Dikko Umaru Radda ya bayyana matukar bakin ciki game da lamarin, yana mai cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da yin aiki kafada da kafada da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro don kawo karshen ayyukan ‘yan fashi da makami da kuma tabbatar da cewa an gurfanar da wadanda suka aikata wannan mummunan aiki a gaban kuliya.



