




Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya halarci liyafar cin abinci (walima) na Hon. Abdullahi Aliyu General (Dujiman Katsina), memba mai wakiltar Musawa/Matazu, wanda aka gudanar a Abuja jiya.
Taron ya samu halartar manyan baki da dama, ciki har da kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajuddeen Abbas; Tsoffin gwamnoni, Rt. Hon. Aminu Bello Masari da Ibrahim Shehu Shema.
Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da ministar fasaha da al’adu, Hannatu Musa Musawa; sanatoci, yan majalisar wakilai, da sauran manyan baki.



