
Gwamnatin jihar Katsina ta dakatar da lasisin gudanar da duk wasu makarantu masu zaman kansu da na al’umma a jihar, daga ranar 13 ga Agusta, 2025.
Sanarwar ta fito ne ta wata takardar da ma’aikatar ilimi ta kasa da sakandire ta fitar mai dauke da sa hannun kwamishina Hajiya Zainab Musa-Musawa.
Jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar, Malam Sani Danjuma, ya fitar da takardar a Katsina ranar Asabar
A cewar sanarwar, matakin wani bangare ne na kokarin gwamnati na karfafa tabbatar da inganci da daidaito a bangaren ilimi.
“Janye lasisin na da nufin tabbatar da cewa makarantu suna aiki daidai da ka’idojin da aka amince da su tare da samar da ingantaccen ilimi ga dalibai,” in ji Danjuma.
Da’idar ta kuma zayyana bitar kudade don neman lasisi, rajista, da sabuntawa na shekara-shekara.
Ana buƙatar masu makarantun da abin ya shafa su sami sabbin lasisi ta hanyar gabatar da shaidar biyan kuɗi ga ma’aikatar a kan ko kafin 30 ga Satumba, 2025.”
Sanarwar ta kuma kara da cewa, an gargadi ma’aikatan makarantar da kada su kara kudin makaranta ko wasu kudade ba tare da amincewar gwamnati ba.
Ma’aikatar ta kuma yi alkawarin fitar da wasu karin ka’idoji nan ba da dadewa ba, wadanda suka hada da rarraba makarantu da tsarin kudaden da aka yi wa kwaskwarima.