
SANARWA
Gwamna Radda Ya Karbawa Gwamna Nasir Idris Bikin Cika Shekaru 60 A Duniya
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bi sahun sauran ‘yan kungiyar Gwamnonin Progressive Governors Forum (PGF) wajen taya Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi Dakta Nasir Idris murnar cika shekaru 60 da haihuwa.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan jihar Katsina Ibrahim Kaula Mohammed ya sanyawa hannu kuma aka mika wa Katsina Mirror.
Gwamna Radda ya bayyana Gwamna Nasir Idris a matsayin jajirtacce, mai hangen nesa, kuma jagora mai kishin kasa wanda ya kawo sauyi mai ma’ana a jihar Kebbi ta hanyar jajircewarsa wajen samar da kyakkyawan shugabanci da yiwa al’umma hidima.
Ya yi nuni da cewa irin ci gaban da Gwamna Idris ya samu a sassa daban-daban da suka hada da samar da ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, bunkasa masana’antu, zaman lafiya da tsaro, da karfafawa jama’a da walwalar jama’a, na nuni da babban kishi na inganta rayuwar al’ummarsa da kuma kafa wani babban shingen shugabanci a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC).
Gwamnan jihar Katsina ya yabawa Gwamna Idris bisa irin rawar da yake takawa a kungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma musamman irin gudunmawar da yake bayarwa wajen karfafa hadin kai da ci gaban kasa a tsakanin Jihohin da APC ke jagoranta.
A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Katsina, Gwamna Radda ya mika sakon gaisuwa ga Gwamna Nasir Idris, inda ya yi addu’ar Allah ya kara masa lafiya, da basira, da kuma ikon ci gaba da jagorancinsa mai tasiri.
Ya yi wa Gwamnan Jihar Kebbi murnar cika shekaru 60 da haihuwa, tare da masoyansa, abokan aikinsa, da kuma masu fatan alheri.