
Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Dutsinma/Kurfi Alhaji Aminu Balele ya bayar da kyautar Sallah ga manyan Limamai da Ladan na masallatan Juma’a na mazabar Dutsinma da Kurfi ta tarayya.
Manyan Limamai sun yabawa dan majalisar bisa wannan karimcin, tare da gode masa da kyaututtukan.
Alh Aminu Balele ya yi kira ga manyan limamai da su yi addu’ar Allah ya kara wa al’umma zaman lafiya da inganta harkar tsaro.
Dan majalisar ya kuma godewa manyan limamai bisa addu’o’in da suke yi na yau da kullum, wanda ya yi imanin cewa an samu sauyi mai kyau a yankin.
Balele Danarewa ya kuma taya shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu murnar nadin jiga-jigan ‘ya’yan jihar guda biyu wato tsohon Gwamna Ibrahim Shehu Shema da Sanata Kabir Abdullahi Barkiya.
Dan majalisar ya godewa Gwamna Dikko Umar Radda da ya taimaka wa wadannan nade-nade.
Alh Aminu Balele ya kuma gana da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC, inda ya gabatar da kyautuka masu tarin yawa na bikin Sallah tare da jan hankalinsu kan amincewa da Gwamna Radda a karo na biyu.