
Gwamnatin jihar Katsina ta jaddada kudirinta na hada kan kananan masana’antu a tsakanin daliban domin dogaro da kai.
Kwamishinan ma’aikatar fasaha da koyar da sana’o’i Alh Isah Muhammad Musa ya bayyana haka a lokacin da yake sa ido kan yadda ake gudanar da jarabawar karshe na daliban B A T C Katsina.
Alh Isah Musa wanda ya bayyana mahimmancin samun sana’o’in hannu, ya bayyana cewa Gwamnatin Gwamna Dikko Ummaru Radda ta tsara tsarin samar da yanayi mai kyau ga kanana da matsakaitan sana’o’i a jihar, ta hanyar samar da ayyukan yi da matasa a fadin kananan hukumomin jihar 34.
Kwamishinan ya ci gaba da cewa gwamnatin jihar ta umurci ‘yan kwangilar da su tabbatar da bada tallafi da kuma siyan kayayyakin da aka kera a cikin gida domin bunkasa kananan sana’o’i ta yadda za a inganta hanyoyin samun kudaden shiga a jihar.
Ya kuma yi kira ga daliban cibiyar da su ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen ganin sun samu kwarewa da kuma shirye su zama masu daukar ma’aikata domin inganta tattalin arzikin jihar.
A nasa jawabin Manajan cibiyar Alh Shuaibu Yusuf ya nuna jin dadinsa ga gwamnatin jiha bisa samar da cibiya mai cike da kayan aiki wadanda suka saukaka ayyukanta.
Ya ba da tabbacin cewa masu koyan cibiyar za su iya samun nasarar gudanar da ayyuka daban-daban tare da kyawawan dabarun zamani na duniya.