
Shugaban Kwamitin Sojoji na Majalisar, Alhaji Aminu Balele Kurfi Danarewa ya ji dadin yadda al’ummar Musulmi suka yi amfani da kwanaki goma na karshen watan Ramadan wajen rokon Allah Ya kawo mana karshen kalubalen tsaro da ke addabar wasu sassan kasar nan.
Alhaji Aminu Dabarewa wanda shi ne dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Dutsinma Kurfi ya yi wannan kiran a sakonsa na watan Ramadan ga al’ummar musulmi.
Dan majalisar ya bayyana kwanaki goman karshe na watan Ramadan a matsayin ranakun da al’ummar musulmi suke amfani da su wajen yin addu’a, karatun littafi mai daraja, yin sallolin dare da sauran ayyukan ibada ga Allah madaukaki.
Ya tunatar da al’ummar mazabarsa da jihar Katsina da ma kasa baki daya cewa gwamnati a dukkan matakai ta himmatu wajen ganin kalubalen tsaro ya zama tarihi.
Alhaji Aminu Danarewa ya roki Allah Madaukakin Sarki da Ya ba mu damar ganin watan Ramadan.